fidelitybank

Masu yankan Aljihu sun shiga hannun ‘yan sanda yayin taron APC

Date:

Jami’an tsaro sun cafke wasu mutum uku da ake zargi da yankan aljihu a wajen babban taron jam’iyar APC da ke gudana a Abuja, bayan kama su suna satar wayar salula a kofar shiga filin taron.

Wani jami’in tsaro ya faɗa wa kamfanin labara na Najeriya NAN cewa waɗanda aka Kama ɗin sun faki idon dandazon mutane da ke kofar shiga filin taron na Eagle Square wajen sace wayoyinsu.

Jami’in tsaron ya kuma ce waɗanda ake zargi da sace wayoyin sun haɗa baki wajen aiki tare, inda suke sace wayoyi da kuma kuɗin mutane da ke filin taron.

Har wa yau, jami’in tsaron ya ce an samu damar kama mutanen ne da taimakon sauran abokan aikinsu ‘yan sanda da ke sanya ido a kofar shiga Eagle Square yayin da wakilai ke shiga domin kaɗa kuri’arsu.

Ya ce za a kai waɗanda ake zargin zuwa shelikwatar ‘yan sanda domin ci gaba da bincike.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp