fidelitybank

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Date:

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga bayanai ne ke haddasa kashi 80 cikin 100 na hare-haren yanbindiga a faɗin jihar.

Kwamishinan tsaro da al’amuran cikin gida na jihar, Nasir Mua’azu ne ya bayyana haka yayin da yake jawabi ga manema labarai a jihar.

Nasir Mu’azu ya ce masu kwarmata wa ƴanbindigar bayanai da ke kai musu abinci da sauran abubuwa ne ke ba su bayanan da suke buƙata domin ƙaddamar da hare-hare.

Kwamishinan ya ce hakan kuma na matuƙar kawo wa gwamnati tsaiko wajen yaƙi da matsalar ƴan fashin daji a faɗin jihar.

Ya ƙara da cewa wasu daga cikin irin waɗannan mutane kan kai wa ƴanbindigar abubuwan da suke buƙata har dazuka su kuma sayar musu a farashi mai tsada.

“A ɗaya daga cikin waɗannan garuruwa an taɓa kama wani mutum na sayar da kwalbar lemo naira 3,000 ga ƴan bindiga, wani kuma na sayar musu man fetur kan naira 5,000 kowace lita”, kamar yadda ya bayyana.

“Haka ma akwai masu kai miyagun ƙwayoyi su sayar musu a farashi mai yawa, sun mayar da hakan sana’ar da suke samun kuɗi masu yawa”, in ji shi.

Kwamishinan ya yi zargin cewa wasu ma daga ciki kan haɗa baki da ƴanbindigar wajen sace mutanen da suke so a sace ciki kuwa har da danginsu.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp