fidelitybank

Masu suka ta akan rufe iyaka sun dawo suna yaba min – Buhari

Date:

Shugaba Muhammadu Buhari ya ce, ƴan Najeriya da suka rika sukarsa saboda rufe iyakokin kasar na kasa daga karshe sun dawo suna yaba masa a kai.

Ya ce ya dauki matakin rufe iyakokin ne domin karfafa wa ƴan Najeriya gwiwa kan samar da abincin da suke bukata.

Shugaban mai barin-gado ya bayyana hakan ne a yau Talata lokacin da yake kaddamar da sabon ginin hedikwatar hukumar hana fasa-kwauri wato kwastan a gundumar Maitama da ke babban birnin tarayyar kasar, Abuja.

Ya ce yana sane ya bayar da umarnin rufe iyakokin saboda ya san ƴan Najeriya suna sayo shinkafa daga waje su ba Nijar da wasu kasashe sannan su shigo da sauran kasar.

Shugaban ya ce da arzikin da Najeriya take da shi tana da mutane da kasa da kuma yanayi, arzikin da kasashe ‘yan kadan ne a duniya suke da shi.

Sai dai ya ce idan aka duba za a ga cewa daga tafkin Chadi zuwa Jamhuriyar Benin akwai nisan sama da kilomita 1,600 saboda haka Allah ne kadai zai iya tsare wannan iyaka da kyau.

”Saboda haka kana bukatar mutumin da yake da karfi da kwarewa ya sa ido a kan wanna aiki,” in ji Buharin.

Shugaban ya ce ya rufe iyakar ne mai tsawon kilomita 1,600 domin ‘yan Najeriya su rika noma abincin da suke bukata, idan kuma ba haka ba sai dai mutum ya mutu.

Ya ce abin da ya sa ya dauki wannan mataki ke nan wanda kuma daga baya an kasar suke yabawa a kai.

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp