fidelitybank

Masu suka ta akan rufe iyaka sun dawo suna yaba min – Buhari

Date:

Shugaba Muhammadu Buhari ya ce, ƴan Najeriya da suka rika sukarsa saboda rufe iyakokin kasar na kasa daga karshe sun dawo suna yaba masa a kai.

Ya ce ya dauki matakin rufe iyakokin ne domin karfafa wa ƴan Najeriya gwiwa kan samar da abincin da suke bukata.

Shugaban mai barin-gado ya bayyana hakan ne a yau Talata lokacin da yake kaddamar da sabon ginin hedikwatar hukumar hana fasa-kwauri wato kwastan a gundumar Maitama da ke babban birnin tarayyar kasar, Abuja.

Ya ce yana sane ya bayar da umarnin rufe iyakokin saboda ya san ƴan Najeriya suna sayo shinkafa daga waje su ba Nijar da wasu kasashe sannan su shigo da sauran kasar.

Shugaban ya ce da arzikin da Najeriya take da shi tana da mutane da kasa da kuma yanayi, arzikin da kasashe ‘yan kadan ne a duniya suke da shi.

Sai dai ya ce idan aka duba za a ga cewa daga tafkin Chadi zuwa Jamhuriyar Benin akwai nisan sama da kilomita 1,600 saboda haka Allah ne kadai zai iya tsare wannan iyaka da kyau.

”Saboda haka kana bukatar mutumin da yake da karfi da kwarewa ya sa ido a kan wanna aiki,” in ji Buharin.

Shugaban ya ce ya rufe iyakar ne mai tsawon kilomita 1,600 domin ‘yan Najeriya su rika noma abincin da suke bukata, idan kuma ba haka ba sai dai mutum ya mutu.

Ya ce abin da ya sa ya dauki wannan mataki ke nan wanda kuma daga baya an kasar suke yabawa a kai.

vanguardnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp