fidelitybank

Masu son yin zanga-zanga kar ku mayar da Najeriya kamar Sudan – Tinubu

Date:

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana fara shirin rancen dalibai, sabon mafi karancin albashi na N70,000 da kuma kafa tsarin bashi na masu amfani a matsayin dalilan da bai kamata ‘yan Najeriya su fara zanga-zangar wahala da ake shirin yi a ranakun 1-10 ga watan Agustan 2024 ba.

Shugaban ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin tawagar shugabannin addinin Musulunci karkashin jagorancin Sheikh Bala Lau, a fadar gwamnati ranar Alhamis.

Tinubu ya bukaci masu shirya zanga-zangar da kada su mayar da Najeriya Sudan.

A cewarsa, gwamnatinsa na sake yin wani shiri na jin dadin jama’a domin kaiwa kowane dan Najeriya mara karfi a matakin farko.

“Muna sake aiwatar da tsarin jin dadin jama’a don isa ga matakin unguwanni, wanda shine mafi kusanci ga mutanenmu. Za mu tabbatar da cewa mun sake kulla alaka da unguwanni, domin mu ba da alawus-alawus ga talakawa da marasa galihu.

“Lamunin dalibai zai biya kudin makaranta. Za a sami tallafin kuɗi don ilimin yaranmu. Lamunin mabukaci zai tallafa wa ’yan ƙasa don siyan motoci da gidaje, kuma za su iya biya a hankali.

“Mun kara mafi karancin albashi da fiye da kashi 100,” in ji shi.

A ranar Laraba ne Majalisar Dokokin Najeriya ta amince da sabuwar dokar mafi karancin albashi bayan Tinubu da ma’aikatan Najeriya sun amince da N70,000 mafi karancin albashi.

Tun a makon da ya gabata ne gwamnatin tarayya ta fara bayar da kudade ga mutane 110,000 da suka ci gajiyar shirin rancen dalibai na Naira biliyan 35.

Wannan na zuwa ne watanni bayan da gwamnatin Tinubu a watan Afrilu ta amince da karbo bashin Naira biliyan 100 ga ‘yan Najeriya.

nnn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp