fidelitybank

Masu sanya ido na kasashen rainon Ingila sun iso Najeriya

Date:

Masu sa ido a zaɓe daga ƙasashen renon ingila sun iso Abuja, babban birnin Najeriya, gabanin babban zaɓen ƙasar na shugaban ƙasa da kuma ‘yan majalisar tarayya a ranar Asabar.

Kungiyar ta kunshi mutum 16 da suka fito daga ƙasashen renon ingila wanda ya kunshi ‘yan siyasa da jami’an diflomasiyya da masana bangaren shari’a da masu kare hakkin ɗan adam da kuma daidaiton jinsi.

Da yake jawabi ga manema labarai a yau Litinin, shugaban kungiyar wada kuma shi ne tsohon shugaban Afirka ta Kudu, Thabo Mbeki, ya ce kudurinsu shi ne sa ido da kuma duba shirin da aka yi kafin zaɓe da ayyukan ranar zaɓe da kuma bayan zaɓe.

Mista Mbeki ya lura da cewa zaɓukan Najeriya za su kasance manya a nahiyar Afirka kuma sakamakonta na da matukar muhimmanci ga ɗaukacin nahiyar.

A don haka ya buƙaci jam’iyyun siyasa a ƙasar da ‘yan takara da kuma magoya bayansu da su tabbatar da ganin an yi zaɓukan ranar 25 ga watan Febrairu cikin koshin lafiya da kuma gaskiya.

An kiyasta cewa mutum miliyan 93.4 ne suka yi rajista domin samun damar kaɗa kuri’a a zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya a cikin rumfunan zaɓe 176,846 da ke faɗin Najeriya.

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp