fidelitybank

Masu motocin dakon man fetur su rinƙa kiyaye dokoki kar irin na Jigawa ya sake faruwa – IGP

Date:

Sufeto-Janar na ‘yan sanda, IGP Kayode Adeolu Egbetokun ya jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar Jigawa bisa mutuwar mutane kusan 140 sakamakon fashewar tankar mai da ta afku a ranar Talata.

Al’ummar Majia da ke karamar hukumar Taura a jihar Jigawa sun jefa cikin rudani a ranar Talatar da ta gabata sakamakon fashewar tankar da ta yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da jikkata wasu da dama.

Ko da yake rundunar ‘yan sandan Jigawa ta bayyana a ranar Laraba cewa mutane 90 ne suka mutu a lamarin, shaidun gani da ido sun ce sama da mutane 140 ne aka binne a ranar Laraba bayan aukuwar lamarin.

Da yake mayar da martani, IGP a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, Olumuyiwa Adejobi ya fitar a ranar Alhamis ya bukaci masu ababen hawa da su rika bin ka’idojin tsaro a kullum.

Ya kuma yabawa kokarin jami’an ‘yan sanda da sauran jami’an agajin gaggawa kan matakin da suka dauka na kashe gobarar, da kwashe wadanda abin ya shafa, da kuma tabbatar da an dawo da zaman lafiya cikin gaggawa a yankin.

IGP, yayin da yake addu’a ga rayukan wadanda suka rasu, ya tabbatar wa da jama’a “tsare-tsare na wayar da kan jama’a game da illolin da ake samu na diban mai da sauran ayyukan makamantansu”.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp