fidelitybank

Masu motocin dakon man fetur su rinƙa kiyaye dokoki kar irin na Jigawa ya sake faruwa – IGP

Date:

Sufeto-Janar na ‘yan sanda, IGP Kayode Adeolu Egbetokun ya jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar Jigawa bisa mutuwar mutane kusan 140 sakamakon fashewar tankar mai da ta afku a ranar Talata.

Al’ummar Majia da ke karamar hukumar Taura a jihar Jigawa sun jefa cikin rudani a ranar Talatar da ta gabata sakamakon fashewar tankar da ta yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da jikkata wasu da dama.

Ko da yake rundunar ‘yan sandan Jigawa ta bayyana a ranar Laraba cewa mutane 90 ne suka mutu a lamarin, shaidun gani da ido sun ce sama da mutane 140 ne aka binne a ranar Laraba bayan aukuwar lamarin.

Da yake mayar da martani, IGP a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, Olumuyiwa Adejobi ya fitar a ranar Alhamis ya bukaci masu ababen hawa da su rika bin ka’idojin tsaro a kullum.

Ya kuma yabawa kokarin jami’an ‘yan sanda da sauran jami’an agajin gaggawa kan matakin da suka dauka na kashe gobarar, da kwashe wadanda abin ya shafa, da kuma tabbatar da an dawo da zaman lafiya cikin gaggawa a yankin.

IGP, yayin da yake addu’a ga rayukan wadanda suka rasu, ya tabbatar wa da jama’a “tsare-tsare na wayar da kan jama’a game da illolin da ake samu na diban mai da sauran ayyukan makamantansu”.

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp