Kungiyar masu kiwon kaji a Najeriya ta koka kan yadda ‘yan Najeriya da dama ba za su iya siyan kwai ba saboda tabarbarewar tattalin arziki.
Hussaini Gumel, kungiyar PFAN reshen jihar Jigawa ne ya bayyana haka a lokacin da suka kai wa gwamna Umar Namadi ziyarar ban girma a ranar Alhamis a gidan gwamnati dake Dutse babban birnin jihar.
A cewar Gumel, “Tun da aka cire tallafin man fetur, masana’antarmu ta shiga tsaka mai wuya, ‘yan Najeriya da dama ba sa iya sayen kwai, kuma tallace-tallacen mu ya yi kasa a gwiwa.”
Ya danganta raguwar tallace-tallacen da karuwar matsalolin tattalin arziki da ‘yan Najeriya da dama ke fuskanta.
“Muna kokawa don ci gaba da kasuwancinmu.
“Babu kasuwar kayayyakinmu, kuma rashin isassun kudade da ke yawo a tsakanin mutane abu ne mai ban tsoro,” in ji Mista Gumel, yana mai gargadin cewa kasuwancin na gab da durkushewa.
Rahotanni na cewa, yanzu haka ana siyar da kwandon kwai a kasuwannin Najeriya tsakanin Naira 5,700 zuwa 6,000, ya danganta da wurin da ake ciki.