Kwamishinan ‘yan sandan jihar Anambra, CP Echeng Echeng, ya ce, rundunar ta kama wasu mutane hudu da ake zargi da hannu wajen karbar kudaden shiga ba bisa ka’ida ba a jihar.
Echeng ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin da yake gabatar da mutanen hudu a ofishin ‘yan sanda da ke Amawabia.
A cewarsa, kokarin da ake yi na kawar da jihar Anambra daga duk wani nau’in yana haifar da sakamako mai kyawu.
Mutanen hudu da ake zargin su ne Emmanuel Igwe, mai shekaru 20; Chukwudi Obasi, 38; Izuchukwu Enemuwa, 28 da Uchenna Benedict, 28.
A cewarsa, an kama wadanda ake zargin ne a ranar Laraba a kan titin Headbridge, Onitsha yayin da suke karbar kudaden shiga ba bisa ka’ida ba daga masu ababen hawa da sauran jama’a.