fidelitybank

Masu jiran hukuncin alkali sun cushe mana gidan yarin Kano – Bursin

Date:

Hukumar da ke lura da gidajen gyaran hali ta kasa reshen jihar Kano, ta nuna damuwa kan ƙaruwar masu zaman jiran shari’a a gidajen yari da ke faɗin jihar.

Wata sanarwa da kakakin hukumar reshen jihar Musbahu Lawan ya fitar, ta ce ƙaruwar mutanen da ke jiran a yanke masu hukunci na kawo wa hukumar cikas wajen gudanar da ayyukanta a jihar, inda ya ce yawan fursunoni masu jiran shari’a ya ninƙa har sau uku idan aka kwatanta da waɗanda aka yanke wa hukunci a jihar.

“Fursunoni ma su zaman shari’a ya kai kashi 70 na ɗaukacin fursunoni da ake da su a faɗin jihar, ana tsare da yawancinsu duk da cewa kotu ba ta kammala yanke hukunci kan shari’o’insu ba,” in ji Musbahu.

Kofar Nasarawa ya ce idan da a ce an yanke wa mutanen da ke zaman jiran shari’a hukunci, to da hukumar ba za ta yi ƙorafi kan cikar gidajen yarin ba, saboda doka ta ba su damar sauya wa fursunonin da aka yanke wa hukunci wurin zama zuwa ko’ina a faɗin ƙasar.

Ya ƙara da cewa an fi samun sauƙin kula da fursunonin da aka yanke wa hukunci saboda ana saka su cikin shirye-shiryen gyaran hali, wani abu da waɗanda ke zaman jiran shari’a ba su da damar morar sa.

Mai magana da yawun gidajen gyaran halin, ya ce wasu fursunoni 38 waɗanda aka yanke wa hukunci sun zana jarrabawar kammala sakandare ta NECO, kuma suna neman gurbin karatu a Jami’ar karatu daga gida (NOUN).

Musbahu ya ce duba da ƙaruwar fursunonin da suka nuna sha’awar karatu, hukumar na aiki da Jami’ar ta NOUN domin kafa ƙarin cibiyoyin karatu a gidajen yari a faɗin jihar.

Ya yaba wa gwamnatin tarayya bisa ɓullo da matakai na yi wa fursunoni afuwa domin shawo kan matsalar cunkoso a gidan gyaran hali.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp