fidelitybank

Masu jiran hukuncin alkali sun cushe mana gidan yarin Kano – Bursin

Date:

Hukumar da ke lura da gidajen gyaran hali ta kasa reshen jihar Kano, ta nuna damuwa kan ƙaruwar masu zaman jiran shari’a a gidajen yari da ke faɗin jihar.

Wata sanarwa da kakakin hukumar reshen jihar Musbahu Lawan ya fitar, ta ce ƙaruwar mutanen da ke jiran a yanke masu hukunci na kawo wa hukumar cikas wajen gudanar da ayyukanta a jihar, inda ya ce yawan fursunoni masu jiran shari’a ya ninƙa har sau uku idan aka kwatanta da waɗanda aka yanke wa hukunci a jihar.

“Fursunoni ma su zaman shari’a ya kai kashi 70 na ɗaukacin fursunoni da ake da su a faɗin jihar, ana tsare da yawancinsu duk da cewa kotu ba ta kammala yanke hukunci kan shari’o’insu ba,” in ji Musbahu.

Kofar Nasarawa ya ce idan da a ce an yanke wa mutanen da ke zaman jiran shari’a hukunci, to da hukumar ba za ta yi ƙorafi kan cikar gidajen yarin ba, saboda doka ta ba su damar sauya wa fursunonin da aka yanke wa hukunci wurin zama zuwa ko’ina a faɗin ƙasar.

Ya ƙara da cewa an fi samun sauƙin kula da fursunonin da aka yanke wa hukunci saboda ana saka su cikin shirye-shiryen gyaran hali, wani abu da waɗanda ke zaman jiran shari’a ba su da damar morar sa.

Mai magana da yawun gidajen gyaran halin, ya ce wasu fursunoni 38 waɗanda aka yanke wa hukunci sun zana jarrabawar kammala sakandare ta NECO, kuma suna neman gurbin karatu a Jami’ar karatu daga gida (NOUN).

Musbahu ya ce duba da ƙaruwar fursunonin da suka nuna sha’awar karatu, hukumar na aiki da Jami’ar ta NOUN domin kafa ƙarin cibiyoyin karatu a gidajen yari a faɗin jihar.

Ya yaba wa gwamnatin tarayya bisa ɓullo da matakai na yi wa fursunoni afuwa domin shawo kan matsalar cunkoso a gidan gyaran hali.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...
X whatsapp