fidelitybank

Masu haɗakar ADC na ɓaɓatu ne saboda rashin gwamnati – Radda

Date:

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umar Radda ya yi watsi da sabuwar haɗakar ƴan hammayar ƙasar, waɗanda ya bayyana da masu haushin rashin gwamnati a hannunsu.

Yayin da yake jawabi a gidan talbijin na Channels ta cikin shirin Sunrise Daily, Gwamnan ya ce shirin haɗakar ADC ba wani abu ne face tsantsar yaudara.

“Ya kamata mu faɗa wa kanmu gaskiya, lokacin yaudarar mutanen Najeriya fa ya ƙare”, in ji shi.

A makon da ya gabata ne gamayyar wasu ƴan hamayya daga jam’iyyu daban-daban suka haɗe kai ƙarƙashin inuwar jam’iyyar ADC da nufin ƙalubalantar gwamnatin APC a 2027.

Ƴan hamayyar sun zargi gwamnatin APC da lalata Najeriya da kuma yunƙurin mayar da ƙasar mai bin tafarkin jam’iyya guda.

To sai dai Gwamnan na Katsina ya ƙalubalanci masu haɗakar da cewa me suka yi wa Najeriya a lokacin da suke riƙe da madafun iko.

“Wane ne a cikinsu ba ya cikin gwamnatin da ta gabata? Waye a cikinsu bai taɓa shiga gwamnati ba? Muna sane da irin abubuwan da kowanensu ya yi,” in ji Gwamnan na Katsina.

“Mun san irin abubuwan da suka yi lokacin da suke gwamnati, sai yanzu za su zo suna ɓaɓatu saboda ba sa cikin gwamnati.” a cewar Gwamna Radda.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

JAMB ta amince da maki 150 mafi ƙanƙanta don samun gurbin karatu a jami’o’i

Hukumar shirya jarrabawar shiga Jami'o'i ta Najeriya (JAMB) ta...

ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Najeriya, ASUU da dakatar yajin...

Masu haɗakar ADC na ɓaɓatu ne saboda rashin gwamnati – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umar Radda ya yi...

Ba ruwan Biri da gada a makamin Nukiliya – Shettima

Mataimakin shugaba Najeriya Kashim Shettima ya ce ƙasar za...

An kashe Mutane 70 a jihar Filato

Rahotonni daga jihar Filato na cewa ƴanbindiga sun kai...

Ambaliya ta kashe mutane 100 a Amurka

Hukumomi a jihar Tesxas da ke Amurka sun bayyana...

Tsohon Ministan kuma jigo a PDP ya koma ADC

Tsohon ministan harkokin ‘yan sanda kuma sau uku a...

Trump ya caccaki Elon Musk

Shugaban Amurka Donald Trump ya caccaki tsohon mashawarcinsa, Elon...

Dalilin da ya sa Kwankwaso ya ki shiga jam’iyyar hadaka – Galadima

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...

Obi ba zai taba zama shugaban kasa ba – Wike

Ministan Abuja, Nyesom Wike ya ce, tsohon ɗan takarar...

Ƴansanda sun kama ƴan Ghana 19 da aka yi safararsu a Najeriya

Rundunar ƴansandan Najeriya ta kuɓutar da wasu ƴan Ghana...

Benue da Edo da Bayelsa na fargabar balewar madatsar ruwan Kamaru

Gwamnatocin jihohi uku na cikin shirin ko-ta -kwana, sakamakon...
X whatsapp