fidelitybank

Masu haɗakar ADC na ɓaɓatu ne saboda rashin gwamnati – Radda

Date:

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umar Radda ya yi watsi da sabuwar haɗakar ƴan hammayar ƙasar, waɗanda ya bayyana da masu haushin rashin gwamnati a hannunsu.

Yayin da yake jawabi a gidan talbijin na Channels ta cikin shirin Sunrise Daily, Gwamnan ya ce shirin haɗakar ADC ba wani abu ne face tsantsar yaudara.

“Ya kamata mu faɗa wa kanmu gaskiya, lokacin yaudarar mutanen Najeriya fa ya ƙare”, in ji shi.

A makon da ya gabata ne gamayyar wasu ƴan hamayya daga jam’iyyu daban-daban suka haɗe kai ƙarƙashin inuwar jam’iyyar ADC da nufin ƙalubalantar gwamnatin APC a 2027.

Ƴan hamayyar sun zargi gwamnatin APC da lalata Najeriya da kuma yunƙurin mayar da ƙasar mai bin tafarkin jam’iyya guda.

To sai dai Gwamnan na Katsina ya ƙalubalanci masu haɗakar da cewa me suka yi wa Najeriya a lokacin da suke riƙe da madafun iko.

“Wane ne a cikinsu ba ya cikin gwamnatin da ta gabata? Waye a cikinsu bai taɓa shiga gwamnati ba? Muna sane da irin abubuwan da kowanensu ya yi,” in ji Gwamnan na Katsina.

“Mun san irin abubuwan da suka yi lokacin da suke gwamnati, sai yanzu za su zo suna ɓaɓatu saboda ba sa cikin gwamnati.” a cewar Gwamna Radda.

assu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp