fidelitybank

Masu gidajen Burodi sun janye yajin aiki

Date:

Ƙungiyar masu gidajen burodi ta kasa (AMBCN) ta bayyana cewa, ta janye yajin aikin da ta shiga bayan wata tattaunawa da ta gudanar da jami’an ma’aikatar noma ta ƙasar.

A cikin wata sanarwa da ta fitar da yammacin ranar Laraba, wadda ta samu sa hannun shugabanta, Mansur Umar, ƙungiyar ta ce ta cimma wasu yarjeniyoyi da gwamnatin Najeriya a tattaunawar tasu, wanda hakan ya sanya ta sanar da janye yajin aikin wanda ta fara a ranar Talata.

Daga cikin yarjejeniyar da aka cimma tsakanin ƙungiyar da gwamnati sun haɗa da fitar da metric tan 25,000 na alkama nan take ga kamfanonin fulawa domin sarrafawa da samar wa masu sana’ar burodi.

Haka nan ɓangarorin biyu sun cimma yarjejeniya kan sake duba shirin samar da fulawa daga rogo da dankali da kuma dawa.

Sannan kuma an cimma yarjejeniyar tallafa wa masu sana’ar ta burodi ƙarƙashin wani shiri na ma’aikatar noma ta Najeriyar.

Masu gidan burodin a Najeriya sun shiga yajin aiki ne bayan kokawa da tsadar farashin kayan aiki, lamarin da ke kawo tarnaƙi a harkar sana’ar tasu.

Najeriya na fama da tashin farashin kayan masarufi, lamarin da ake dangantawa da cire tallafin man fetur a ƙasar da kuma wanu manufofi na gwamnati.

legitnews.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp