fidelitybank

Masu garkuwa sun hallaka wani dan kasuwa a Ondo

Date:

A karshen makon da ya gabata ne wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka yi garkuwa da Augustine Okoye, wani dan kasuwa a Ugbe da ke karamar hukumar Akoko ta Arewa maso Gabas a jihar Ondo.

Marigayin, shahararren mai sayar da kayan shafawa a yankin Ikare-Akoko na jihar an ce an kashe shi ne bayan an biya kudin fansa da ba a bayyana ba.

An dai sace Okoye da matarsa ne a kan babbar hanyar Isua-Ise Akoko a kan hanyarsu ta zuwa garin Isua.

Masu garkuwa da mutanen sun sako matar tare da kashe dan kasuwan bayan sun karbi kudin fansa daga danginsu.

Da take bayyana yadda aka sace su, matar, Bolaji Augustine, ta bayyana cewa an kashe Okoye kafin a biya kudin fansa.

Yayin da yake tabbatar da faruwar lamarin, wata majiyar ‘yan sanda a Ikare Akoko ta ce an gano motar da aka yi amfani da ita wajen sace mutanen daga wurin da lamarin ya faru.

Majiyar ‘yan sandan ta kara da cewa jami’an hukumar Amotekun da ’yan banga a yankin sun fara tseratar dajin domin kwato gawar Okoye tare da cafke wadanda ake zargin.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp