fidelitybank

Masu garkuwa sun hallaka wani dan kasuwa a Ondo

Date:

A karshen makon da ya gabata ne wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka yi garkuwa da Augustine Okoye, wani dan kasuwa a Ugbe da ke karamar hukumar Akoko ta Arewa maso Gabas a jihar Ondo.

Marigayin, shahararren mai sayar da kayan shafawa a yankin Ikare-Akoko na jihar an ce an kashe shi ne bayan an biya kudin fansa da ba a bayyana ba.

An dai sace Okoye da matarsa ne a kan babbar hanyar Isua-Ise Akoko a kan hanyarsu ta zuwa garin Isua.

Masu garkuwa da mutanen sun sako matar tare da kashe dan kasuwan bayan sun karbi kudin fansa daga danginsu.

Da take bayyana yadda aka sace su, matar, Bolaji Augustine, ta bayyana cewa an kashe Okoye kafin a biya kudin fansa.

Yayin da yake tabbatar da faruwar lamarin, wata majiyar ‘yan sanda a Ikare Akoko ta ce an gano motar da aka yi amfani da ita wajen sace mutanen daga wurin da lamarin ya faru.

Majiyar ‘yan sandan ta kara da cewa jami’an hukumar Amotekun da ’yan banga a yankin sun fara tseratar dajin domin kwato gawar Okoye tare da cafke wadanda ake zargin.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp