fidelitybank

Masu garkuwa na neman Naira miliyan 50 don sakin tsohon sakataren hukumar NNF

Date:

Masu garkuwa da tsohon sakataren hukumar kwallon kafa ta ƙasa (NFF), Sani Toro da tsohon mataimakin Kociyan Super Eagles, Garba Yila da daya daga cikin abokansu Isa Jah, na neman a sako su akan Naira miliyan 150.

Rahotanni sun bayyana cewa, Toro da wasu sun bar daurin auren dan gidan tsohon shugaban NFF, Aminu Maigari a Abuja ranar Asabar, da misalin karfe 05:00 na yamma a kan hanyarsu ta zuwa Bauchi, inda aka yi garkuwa da su da misalin karfe 07:00 na dare a jihar Nasarawa.

Wata majiya ta iyali ta ce masu garkuwa da mutanen sun bukaci N150m a matsayin kudin fansa.

“Eh, gaskiya ne shi (Isa Toro) yana tuki tare da abokansa guda biyu lokacin da aka yi garkuwa da su jiya (Asabar). Masu garkuwa da mutane suna neman kudin fansa naira miliyan 50 ga kowannen su”, majiyar ta kara da cewa masu garkuwan sun zanta da mai gidan nasu, Maigari.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi Ahmed Wakili ya tabbatar da faruwar lamarin.

Wakili, ya ce: “Labarin gaskiya ne. Na ci karo da daya daga cikin ‘ya’yansa, wanda ya shaida min cewa, an yi garkuwa da shi ne a hanyar Akwanga a Nasarawa a lokacin da yake dawowa daga Abuja.”

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp