fidelitybank

Masu garkuwa da daliban Ekiti sun yi babban barazana

Date:

Shugaban makarantar Apostolic Faith Group inda aka sace dalibai biyar da malamai hudu a jihar Ekiti, ya ce masu garkuwa sun yi barazanar ɗaukan mataki kan mutanen da suka sace idan aka gaza biyan kudin fansar da suka nema.

Gabriel Adesanya ya shaida wa BBC cewa akwai kimanin dalibai 20 da ke cikin motar lokacin da masu garkuwar suka kai musu hari.

Ya ƙara da cewa, “da yawa daga cikin iyayen yaran ba su da ko kashi daya cikin goma na kudin. Yanayi ne na ban tausayi ga makarantar da kuma al’ummar yankin. Har yanzu ba mu cigaba da karatu ba tun bayan kai harin”.

Ɗaya daga cikin daliban da ke cikin motar lokacin da aka kai harin a ranar Litinin ya shaida wa BBC cewa lamarin ya faru bayan an tashi daga makaranta.

Ya ƙara da cewa masu garkuwar sun umarce su da su fito daga motar daga nan suka zaɓi waɗanda za su dauka suka tafi tare dasu.

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya umarci a yi gaggawar ceto mutanen inda ya ba da tabbacin hakan ba za ta ƙara faruwa ba.

A halin yanzu an buƙaci shugabannin tsaro da su gurfana a gaban majalisar dattawa ta kasa a mako mai zuwa domin tattaunawa game da karuwar rashin tsaro da ake fuskanta a kasar.

Yin garkuwa da mutane don karɓar kuɗin fansa na kara tsananta a Najeriya cikin shekarun baya-bayan nan inda yan bindiga ke kai farmaki ga mutane masu tafiya a mota da ɗalibai har ma da mazauna ƙarkara da wasu wuraren a biranen da ke sassan ƙasar.

tribune newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp