fidelitybank

Masu garkuwa da daliban Ekiti sun yi babban barazana

Date:

Shugaban makarantar Apostolic Faith Group inda aka sace dalibai biyar da malamai hudu a jihar Ekiti, ya ce masu garkuwa sun yi barazanar ɗaukan mataki kan mutanen da suka sace idan aka gaza biyan kudin fansar da suka nema.

Gabriel Adesanya ya shaida wa BBC cewa akwai kimanin dalibai 20 da ke cikin motar lokacin da masu garkuwar suka kai musu hari.

Ya ƙara da cewa, “da yawa daga cikin iyayen yaran ba su da ko kashi daya cikin goma na kudin. Yanayi ne na ban tausayi ga makarantar da kuma al’ummar yankin. Har yanzu ba mu cigaba da karatu ba tun bayan kai harin”.

Ɗaya daga cikin daliban da ke cikin motar lokacin da aka kai harin a ranar Litinin ya shaida wa BBC cewa lamarin ya faru bayan an tashi daga makaranta.

Ya ƙara da cewa masu garkuwar sun umarce su da su fito daga motar daga nan suka zaɓi waɗanda za su dauka suka tafi tare dasu.

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya umarci a yi gaggawar ceto mutanen inda ya ba da tabbacin hakan ba za ta ƙara faruwa ba.

A halin yanzu an buƙaci shugabannin tsaro da su gurfana a gaban majalisar dattawa ta kasa a mako mai zuwa domin tattaunawa game da karuwar rashin tsaro da ake fuskanta a kasar.

Yin garkuwa da mutane don karɓar kuɗin fansa na kara tsananta a Najeriya cikin shekarun baya-bayan nan inda yan bindiga ke kai farmaki ga mutane masu tafiya a mota da ɗalibai har ma da mazauna ƙarkara da wasu wuraren a biranen da ke sassan ƙasar.

latest news in nigeria today 2022 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...
X whatsapp