fidelitybank

Masu cin naman mutum da siyarwa a Zamfara sun shiga hannun hukuma

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta kama mutum hudu da zargin sayar da naman sassan jikin dan Adam tare da ci wanda wani abu da ba a saba gani ba a jihar.

A taron manema labarai da ya gudanar a Gusau babban birnin jihar ta Zamfara ranar Alhamis, Kwamishinan ‘yan sanda Ayuba Elkana ya ce, an damke wadanda ake zargin ne bayan da jami’an tsaro suka tsinci gawa a wani kango, ba tare da wasu sassan jikinta ba.

Gano gawar wani bangare ne na bincike da ake yi kan batan wani yaro dan shekara tara.

BBC ta rawaito cewa, tun a makon da ya gabata aka ma mutanen hudu da a ke zargi, da suka hada da wasu magidanta maza biyu da kuma matasa suma maza biyu kamar yadda CP Elkana ya sanar.

Ya kara da cewa yanzu haka ana kan neman wasu mambobin kungiyar da ake zargi da cin naman mutane.

Kazalika kwamishinan ‘yan sandan ya ce kawo yanzu bincike ya nuna cewa sau biyu shugaban kungiyar na tura wa uku daga cikin wadanda aka kama naira 500,000 na cinikin sassan jikin dan adam.

Cin nama da sayar da sassan jikin mutane wani sabon abu ne a Zamfara, duk da jihar ta yi kaurin suna wurin kashe-kashe da garkuwa da mutane don neman kudin fansa daga ‘yan bindiga tsawon shekaru.

Kuma hukumomin Najeriya na shan suka saboda nuna gazawa wurin shawo kan halin da jihar ke ciki.

A wata mai kama da haka yayin zantawa da manema labaran CP Ayuba Elkana ya ce jam’ian tsaro sun kubutar da mutun 17 da aka sato daga jihar Neja aka shiga da su Zamfara.

Ya kara da cewa yayin wani sintiri, ‘yan sanda sun kwato makamai da suka hada da bindigar harba makamin roka, bayan bata kashi da ‘yan bindiga a wani daji da ke yankin.

A makon da ya gabata ne ‘yan fashin daji suka kashe kusan mutun 200, a lokacin da suka kai wasu jerin hare-hare a kauyukan kananan hukumomin Anka da Bukkuyum.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp