fidelitybank

Masu cin naman mutum da siyarwa a Zamfara sun shiga hannun hukuma

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta kama mutum hudu da zargin sayar da naman sassan jikin dan Adam tare da ci wanda wani abu da ba a saba gani ba a jihar.

A taron manema labarai da ya gudanar a Gusau babban birnin jihar ta Zamfara ranar Alhamis, Kwamishinan ‘yan sanda Ayuba Elkana ya ce, an damke wadanda ake zargin ne bayan da jami’an tsaro suka tsinci gawa a wani kango, ba tare da wasu sassan jikinta ba.

Gano gawar wani bangare ne na bincike da ake yi kan batan wani yaro dan shekara tara.

BBC ta rawaito cewa, tun a makon da ya gabata aka ma mutanen hudu da a ke zargi, da suka hada da wasu magidanta maza biyu da kuma matasa suma maza biyu kamar yadda CP Elkana ya sanar.

Ya kara da cewa yanzu haka ana kan neman wasu mambobin kungiyar da ake zargi da cin naman mutane.

Kazalika kwamishinan ‘yan sandan ya ce kawo yanzu bincike ya nuna cewa sau biyu shugaban kungiyar na tura wa uku daga cikin wadanda aka kama naira 500,000 na cinikin sassan jikin dan adam.

Cin nama da sayar da sassan jikin mutane wani sabon abu ne a Zamfara, duk da jihar ta yi kaurin suna wurin kashe-kashe da garkuwa da mutane don neman kudin fansa daga ‘yan bindiga tsawon shekaru.

Kuma hukumomin Najeriya na shan suka saboda nuna gazawa wurin shawo kan halin da jihar ke ciki.

A wata mai kama da haka yayin zantawa da manema labaran CP Ayuba Elkana ya ce jam’ian tsaro sun kubutar da mutun 17 da aka sato daga jihar Neja aka shiga da su Zamfara.

Ya kara da cewa yayin wani sintiri, ‘yan sanda sun kwato makamai da suka hada da bindigar harba makamin roka, bayan bata kashi da ‘yan bindiga a wani daji da ke yankin.

A makon da ya gabata ne ‘yan fashin daji suka kashe kusan mutun 200, a lokacin da suka kai wasu jerin hare-hare a kauyukan kananan hukumomin Anka da Bukkuyum.

www.legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuÉ—in gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuÉ—in gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuÉ—a

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiÉ—a wa Isra'ila wasu...
X whatsapp