fidelitybank

Masu bukata ta musamman sun mika kokan baransu ga gwamnati

Date:

Kungiyar masu bukata ta musamman ta kasa, ta yi kira ga gwamnati da ma sauran masu ruwa da tsaki a kan a biya mata wasu muradunsu guda uku.

Kungiyar ta yi kiran ne a wajen wani taron ranar tunawa da masu bukata ta musamman da aka yi a Abuja babban birnin tarayya.

Kungiyar ta shaida wa BBC cewa, abubuwan da ta ke so a biya mata bukatun a kansu sun hadar da shigar da mutanensu cikin tsare-tsaren bangaren bankuna da ma sabbin tsare-tsaren da Babban Bankin Kasar ya kawo a kwanan nan.

Shugaban kungiyar Isiyaku Adamu Gombe, ya ce, ko kadan Babban Bankin Najeriya ba ya la’akari da wasu daga cikinsu musamman marasa gani idan zai bullo da wasu tsare-tsare.

Ya ce, a don haka suke so gwamnatin tarayya ta sa a rinka tunawa da su a dukkan wani abu da za a fito da shi sabo.

Abu na biyu da kungiyar ta bukaci gwamnati ta yi mata shi ne batun dokar hakkin mallakar da ke gaban majalisa a yanzu, suna bukatar shugaban kasa ya sanya hannu a kai saboda akwai abin da ya shafi mutane masu bukata ta musamman a ciki.

Sai abu na uku da kungiyar ta ce tana so a yi mata shi ne, ‘yan takara da jam’iyyun Najeriya su rinka sanya manufofi na masu bukata ta musamman a dukkanin manufofin da suke son yi wa kasa ko jiha.

Isiyaku Adamu Gombe, ya ce suna da bukatu da suke so a cika musu a don haka suna so su ji manufofin ‘yan takara don su san wadanda za su zaba.

Kidididga ta nuna cewa mutane masu bukata ta mussamman a Najeriya sun kai kashi 15 cikin dari na al’ummar kasar, wato kimanin mutane sama da milyan 30 ke nan.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naÉ—in...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa Æ´an wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...
X whatsapp