Firaministan Burtaniya, Boris Johnson, ya ce, zai cigaba da kare kansa duk da matsin lamba da yake fuskanta na ya sauka daga mulki.
Wani ƙusa a jam’iyar Conservative da ya juya masa baya, Davis Davis, wanda ya bukaci Boris Johnson tare da hadashi da Allah da ya amsa laifinsa ya kuma sauka.
Shi ma jagoran adawa Kier Stammer, ya ce, Mista Johnson na yi wa ‘yan kasar kallon wawaye ko kuma ba su san me suke yi ba.
Sai dai Firaministan, ya ce, ya kamata masu adawa su jira a fitar da sakamakon bincike kafin su yanke hukunci.
A na neman amincewar ‘yan majalisa 54 ne kafin a iya gabatar da kudurin tsige Firaministan.