Mataimakin Shugaban Jam’iyyar Labour (LP), Favor Reuben, ya ce, mutanen da ke adawa da dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Peter Obi, suna adawa da ci gaban Najeriya.
Reuben dai na mayar da martani ne kan matakin da jam’iyyar LP ta dauka na baya-bayan nan a yankin Arewa maso Yammacin kasar nan, inda suka ruguza tsarinsu domin marawa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress, APC, Bola Tinubu baya.
Ya ce mutanen da ke adawa da takarar Obi su ne wadanda ke da tsarin aikata laifuka da rashawa.
“Kamar yadda nake magana da ku, har ’yan Arewa suna goyon bayansa, kowa yana goyon bayansa.
Karanta Wannan: Jam’iyyar LP ta na yi wa Tinubu sharar fagge ne kawai – APC
“Mutanen da ba za su iya amincewa da Peter Obi ba su ne mutane masu cin hanci da rashawa, mutanen da suka yanke shawarar ruguza kasar nan, mutanen da suka yanke shawarar cewa wahala ta zama hanyar kasar nan. Wannan su ne kawai mutanen da ba za su iya amincewa da Peter Obi ba, ”in ji shi.
A ranar Lahadin da ta gabata ne jam’iyyar LP a yankin Arewa maso yammacin kasar nan, ta ruguza tsarin jam’iyyarsu domin marawa Tinubu baya.