fidelitybank

Masu ɗaga tutar Rasha a zanga-zanga akwai babbar matsala – Bukarti

Date:

Daruruwan masu zanga-zanga sun bi titunan yawancin jihohin arewacin Najeriya da kuma Legas, a yayin da aka shiga rana ta biyar da fara zanga-zangar kuncin rayuwa a kasar.

An ga wasu masu zanga-zangar sun sake haduwa a wasu bangarori na Abuja da kuma Fatakwal da ke kudancin Najeriya.

A wasu jihohin arewa maso yammacin Najeriyar da suka hada da Zamfara da kuma Kaduna, an samu fitowar masu zanga-zangar da dama a yau Litinin inda har wasunsu ke daga tutar Rasha.

Akwai wasu faifayen bidiyo da aka yada a shafukan sada zumunta da ke nuna yadda wasu masu zanga-zangar ke rike da tutar Rasha tare da nuna damuwa a kan karuwar matsalar tsaro a yankunansu.

Ba a san dalilin kawo Rasha cikin zanga-zangar ba, to amma ana fargabar za a iya bai wa lamarin wata fassara ta daban.

Wasu masu sharhi a Najeriya, kamar Bulama Bukarti, sun yi gargadin cewa yawaitar amfani da tutar Rasha a zanga-zangar akwai babbar matsala.

Cikin shafinsa na X , Bukarti ya ce, “Ina bukatar masu zanga-zangar da su yi taka tsan-tsan,sannan kuma kada su bari wasu masu mummunar manufa su yi amfani da su wajen cimma mummunar manufarsu.”

A ranar Lahadi ne shugaban Najeriyar Bola Tinubu, ya gabatar da jawabi ga ‘yan kasar inda ya yi kira ga masu zanga-zangar kuncin rayuwar da su dakatar, abin da wadanda suka shiryata suka ce shugaban kasar bai tabo batutuwan da suke bukata ba a yayin jawabin nasa abin da ya kara tunzurasu ke nan.

vanguardnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp