fidelitybank

Masoya sun cika ofishin Jonathan su na roƙon shi ya fito takarar shugabancin ƙasa

Date:

 

 

 

Ɗaruruwan magoya baya, da su ka haɗa da matasa da gungun mata ne a yau Juma’a su ka yi tsinke a ofishin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Ebele Jonathan.

Magoya bayan, wandanda su ka cika ofishin nasa ɗauke da kwalaye masu ɗauke da sakonni daban-daban, sun yi kira a gare shi da ya fito takarar shugabancin ƙasa a 2023.

Tun misalin ƙarfe 8 na safe ne dai magoya bayan su ka isa ofishin na Jonathan ɗauke da kayan kida, inda su ke ta rera wakoki na goyon baya iri-iri.

Sun nuna takaicin su cewa tun da Jonathan ya bar mulki, yunwa, talauci, rashin tsaro da rashin aikin yi sun yi wa ƙasar katutu.

Masoyan na Jonathan sun ce al’ummar ƙasa, maza da mata sun zama almajirai sabo da irin tsauraran manufofin gwamnti mai ci.

Jaridar PlatinumPost ta rawnaito cewa tuni da fastocin Jonathan na takara su ka cika wasu sassa na Abuja, bayan da shi kuma ya kame bakinsa game da batun tsaya wa takara.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...

Ni da Wike tif da taya ne – Fubara

Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya ce, babu...

Za a yi jana’izar Dantata a ranar Litinin

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid,...

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...
X whatsapp