fidelitybank

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Date:

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman ga gwamna Abba Kabir Yusuf a ma’aikatar tarihi da al’adu ta jihar Kano, ya rasu sakamakon raunukan da ya samu a wani mummunan hari da wasu ‘yan daba suka kai.

Ya rasu ne da safiyar yau a Asibitin kwararru na Murtala Muhammad, kwanaki da dama bayan da wasu ‘yan daba suka yi masa mummunan hari a gidansa inda suka yi masa mummunar raunika.

Harin da aka kai a daren Lahadi ya haifar da zaman makoki a tsakanin abokan aikinsa, abokansa, da abokan siyasa, yayin da ake ci gaba da yin kiraye-kirayen a yi adalci tare da gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Wani makusancin marigayin Mujtaba Muhammad Auwal ne ya tabbatar wa DAILY POST rasuwar a wata tattaunawa da suka yi da shi.

“Gaskiya ne, ya rasu, yanayinsa ya kara tsananta jiya, kuma yau an shirya wani tiyatar – amma Allah bai so ba,” Mujtaba ya fada cikin kuka.

Ya kara da cewa, “Wasu ‘yan baranda ne suka shiga gidansa a daren Lahadi, inda suka caka masa wuka tare da sace masa wayoyinsa,” in ji shi a cikin kuka.

Rahotannin farko a ranar Litinin sun nuna cewa wasu da ake zargin sun sace wayar ne suka kai farmaki gidan Sadiq da dare, inda suka kai masa hari da wuka kafin su gudu da kayansa.

Hare-haren da ake kai wa a lokacin sace-sacen wayar tarho ya zama ruwan dare a Kano, duk da kokarin da hukumomi ke yi na dakile matsalar. A cikin makon nan ne wasu ‘yan fashin waya suka kashe wani dalibin jami’ar Bayero a unguwar Dorayi da ke karamar hukumar Gwale.

Har yanzu dai hukumomi ba su fitar da wata sanarwa a hukumance dangane da kisan Sadiq Gentle ba.

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp