fidelitybank

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Date:

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman ga gwamna Abba Kabir Yusuf a ma’aikatar tarihi da al’adu ta jihar Kano, ya rasu sakamakon raunukan da ya samu a wani mummunan hari da wasu ‘yan daba suka kai.

Ya rasu ne da safiyar yau a Asibitin kwararru na Murtala Muhammad, kwanaki da dama bayan da wasu ‘yan daba suka yi masa mummunan hari a gidansa inda suka yi masa mummunar raunika.

Harin da aka kai a daren Lahadi ya haifar da zaman makoki a tsakanin abokan aikinsa, abokansa, da abokan siyasa, yayin da ake ci gaba da yin kiraye-kirayen a yi adalci tare da gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Wani makusancin marigayin Mujtaba Muhammad Auwal ne ya tabbatar wa DAILY POST rasuwar a wata tattaunawa da suka yi da shi.

“Gaskiya ne, ya rasu, yanayinsa ya kara tsananta jiya, kuma yau an shirya wani tiyatar – amma Allah bai so ba,” Mujtaba ya fada cikin kuka.

Ya kara da cewa, “Wasu ‘yan baranda ne suka shiga gidansa a daren Lahadi, inda suka caka masa wuka tare da sace masa wayoyinsa,” in ji shi a cikin kuka.

Rahotannin farko a ranar Litinin sun nuna cewa wasu da ake zargin sun sace wayar ne suka kai farmaki gidan Sadiq da dare, inda suka kai masa hari da wuka kafin su gudu da kayansa.

Hare-haren da ake kai wa a lokacin sace-sacen wayar tarho ya zama ruwan dare a Kano, duk da kokarin da hukumomi ke yi na dakile matsalar. A cikin makon nan ne wasu ‘yan fashin waya suka kashe wani dalibin jami’ar Bayero a unguwar Dorayi da ke karamar hukumar Gwale.

Har yanzu dai hukumomi ba su fitar da wata sanarwa a hukumance dangane da kisan Sadiq Gentle ba.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp