fidelitybank

Mashako ta kashe yara uku a Kaduna

Date:

Cutar Mashaƙo ta halaka ƙananan yara uku tare da kwantar da bakwai a asibiti, bayan ɓarkewarta a ƙaramar hukumar Maƙarfi da ke jihar Kaduna.

Kamfanin dillancin labaran ƙasar NAN, ya ambato sakataren lafiya na ƙaramar hukumar Makarfi Malam Aliyu Alassan na tabbatar da haka a lokacin zanatawa da shi.

Ya an samu ɓuallar cutar a garin Tashar Na Kawu da ke mazaɓar Gubuchi a ƙaramar hukumar.

Alassan ya ce mafiya yawan waɗanda cutar ta kama ƙananan yara ne, ya ci gaba da cewa tuni aka ɗauki samfurin jininsu tare da aika shi Abuja babban birnin ƙasar domin yin gwaji don tantance cutar .

“An kai waɗanda ake zargi sun kamu da cutar zuwa asibiti, tare da killace su domin ba su kulawar da ta dace”, in ji shi.

Ma’aikatar lafiyar jihar ta tabbatar da ɓullar cutar a wasu garuruwan Kafancan da ke yankin ƙaramar hukumar Jema’a, bayan bayyanar alamomin cutar a wasu unguwanni a garin na kafancan

Cikin wata sanarwa da ya fitar gwamnan jihar Sanata Uba Sani ya umarci ma’aikatar lafiyar jihar da ta gaggauta tura tawagar likitoci zuwa garin na Kafancan domin gudanar da bincike tare da ɗaukar matakan da suka dace kan ɓullar cutar.

A baya-bayan nan cutar mashaƙo na ci gaba da ɓulla a wasu jihohin ƙasar, tare da rahotonnin rasa rayuka masu yawa a wasu jihohin.

Alamomin cutar sun haɗar da wahalar numfashi, da zazzaɓi mai zafi, da tari, da kasala, da zafin maƙogoro da kuma kumburin wuya.

nigeria legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...
X whatsapp