fidelitybank

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Date:

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga makaranta domin aurar da ita kafin ta kammala karatun firamare.
Sanarwar da sakataren yada labaran masarautar, Nasiru Habu Faragai, ya aike da manema labarai a Jumu’ar nan,
Ya ce Sarkin Rano, Ambasada Dakta Muhammad Isa Umaru, ya bayyana hakan ranar Alhamis, yayin bikin ƙaddamar da ɗaukar sababbin daliban aji ɗaya na shekara ta 2025/2026, wanda Hukumar Ilimin Bai ɗaya ta Jiha (SUBEB), tare da haɗin gwiwar UBEC da UNICEF, suka shirya a garin Lausu da ke masarautar Ranon.
Sanarwar ta ce Sarkin ya umarci dagatai, masu unguwanni, sarakunan Fulani da limamai da su tabbatar da bin wannan doka, tare da gargadin cewa duk wanda ya saba mata za a ɗauki matakin ladabtarwa a kansa.
Haka kuma, Sarkin ya gargadi iyaye da malamai da kan su guji hada baki wajen cire yarinya daga makaranta don yi mata aure, yana mai cewa wannan mataki ne da zai hana ci gaban rayuwar yara.
Sarkin ya bukaci iyaye da shugabannin al’umma su ba da haɗin kai da goyon bayan da ake buƙata ga gwamnati a ƙoƙarinta na inganta ilimi a jihar Kano.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...

Barau ya jagorancin gangamin zaben cike gurbi a Kano

Barau ya samu rakiyar Karamin Ministan Gidaje da Raya...

Gwamnatin Kano ta kara fadada shirin matasa 

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya sake,...

An kaiwa Malamin addini hari a Kano bayan an jikatasu da Matarsa

Wani malamin addinin Musulunci, Malam Kabir Idris, da matarsa...

Kotun Kano ta daure wata Mata da ake zargin ta tsafe su

Kotun Majistiri mai lamba 7 da ke Nomansland, ƙarƙashin...

Dalibi ya kashe kansa a cikin Jami’a

Hukumar jami'ar Obafemi Awolowo da ke jihar Osun, sun...

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...
X whatsapp