Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari, ya sake nada wasu daga cikin mambobin majalisarsa da suka ajiye mukamansu, domin tsayawa takara a zaben fidda gwani na jamâiyyar All Progressives Congress (APC) da aka gudanar kwanan nan a mukamai daban-daban.
Wadanda aka sake nada sun hada da kwamishinan kasafin kudi da tsare-tsare na tattalin arziki, Farouk Lawal Jobe, da takwaransa na raya karkara, Mustapha Mahmud, wadanda dukkansu suka tsaya takarar neman tikitin takarar gwamnan jihar amma kuma ya sha kaye.
Mataimakin gwamnan jihar, Mannir Yakubu, ya kuma mayar da mukaminsa na kwamishinan noma.
Sauran âyan majalisar da aka sake nada sun hada da mai ba da shawara na musamman kan harkokin siyasa, Kabir Shaibu, wanda ya tsaya takarar tikitin takarar Sanatan Katsina ta tsakiya; da kuma mai ba da shawara na musamman kan bunkasa tattalin arziki, Abdulkadir Mamman Nasir, wanda ya tsaya takarar tikitin takarar majalisar wakilai ta mazabar Malumfashi/Kafur.
A cikin jawabinsa, Masari ya ce, âSuna nan a cikinmu a duk inda suke. Don haka, muna jin abin da ya fi dacewa a yi shi ne mu nemi su dawo kuma sun amince su ci gaba daga inda suka tsaya.