fidelitybank

Masari ya kafa kwamiti wanda zai binciki kisan da aka yi wa ‘yan sa kai

Date:

Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari, ya kafa kwamiti mai mambobi 13 da zai gudanar da bincike kan kisan ‘yan sa kai sama da 100 da aka yi a wasu garuruwan ƙananan hukumomin Kankara da Bakori a jihar.

A wata sanarwa da daraktan yaɗa labaran gwamnan Al-amin Isa, ya aike wa manema labarai, ya ce ana sa ran kwamitin ƙarkashin jagorancin Hon. Justice A.B. Abdullahi, zai gudanar da bincike domin gano abun da ya haddasa kashe-kashen a waɗannan garuruwa.

Sauran ayyukan da ake sa ran kamitin zai gudanar sun haɗa da yin bincike domin gano adadin rayuka da dukiyoyin da ka rasa a lokacin kashe-kashen.

Tare da gano yawan mutanen da harin ya shafa sannan da gano ƙungiyoyi ko mutanen da ke da suka aikata ko suke da hannu wajen wannan aika-aika.

Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnati na duba yiyuwar tallafa wa waɗanda lamarin ya rusta da su tare da iyalan mamatan, da bayar da shawarar ɗaukar matakan kare kai da bai saɓa wa doka ba, tare da ɗaukar matakai domin kare aukuwar makamancin wannan hari a nan gaba a jihar.

A makon da ya gabata ne dai rahotonni suka ce ‘yan bindiga sun yi wa wasu ‘yan sakai waɗanda ke ƙoƙarin ƙwato wasu shanun sata, kwanton ɓauna tare da kashe sama da 100 a wasu garuruwa a ƙananan hukumomin Kankara da Bakori a jihar.

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp