Mazauna jihar Katsina sun bukaci Gwamna Aminu Masari da ya kammala aikin karkashin kasa da ake yi a cikin babban birni a kan kari domin bunkasa ci gaba.
Ibrahim Suleiman, daya daga cikin mazauna yankin da suka nuna sha’awar hanyar, ya shaidawa manema labarai cewa, za a inganta zirga-zirgar ababen hawa idan an kammala aikin.
Suleiman ya ce, aikin zai inganta zirga-zirgar ababen hawa a garin da kuma inganta zamantakewa da tattalin arziki. Ya yi nuni da cewa hanyar karkashin kasa ita ce hanyar da mutane ke shigowa cikin garin Katsina da sauran wurare.
Wata mazauniya Ladi Balarabe, daga Kofar Kwaya ta ce hanyar karkashin kasa za ta saukaka jigilar kayayyaki da mutane tare da kawata garin.
Mista Masari dai ya bayar da kwangilar aikin gina hanyar karkashin kasa kimanin watanni shida da suka gabata, inda ya yi alkawarin kammala aikin cikin shekara daya.
Gwamnan ya ce, manufar hanyar ita ce rage cunkoson ababen hawa tare da samar da hanyar shiga cikin sauki a cikin garin. In ji Pepople Gazette.