Masarautar Saudiyya ta ɗage dokar hana zirga-zirgar jiragen sama daga Najeriya da wasu kasashe 16.
Sauran kasashe sun hada da Afirka ta Kudu, Namibiya, Botswana, Zimbabwe, Lesotho, Eswatini, Mozambique, Malawi, Mauritius, Zambia, Madagascar, Angola, Seychelles, Jamhuriyyar Comoros, Habasha da Afghanistan.
Sabon tashar Lafia zai zama cibiyar watsa labarai ta Najeriya -NDPHC
Hakazalika, mahukuntan Saudiyya sun kawo karshen bayar da tazara ga jama’a a cikin masallatai biyu masu tsarki a cikin masarautar, amma sun dage da rufe hanci da baki, yayin da suke isa wurin ibada.
Hakan dai na zuwa ne a bisa wata umarni da ma’aikatar harkokin cikin gida ta Saudiyya ta fitar, kuma mai taimaka wa shugaban kasa Muhammadu Buhari kan sabbin kafafen yada labarai, Bashir Ahmad ya tabbatar a shafin Twitter.
Saudi Gazette ta ba da rahoton cewa, matafiya ba za su ƙara yin keɓewar COVID-19 na tilas ba idan sun isa Masarautar.
Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta kasa (GACA) a kasar Saudiyya ta tabbatar da dakatar da zirga-zirgar jiragen sama zuwa Najeriya a wata takardar da ta aikewa dukkan kamfanonin jiragen sama da ke aiki a Saudiyya a ranar 8 ga watan Disamba, 2021.
A watan Janairun 2022, Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bukaci Saudiyya da ta dage takunkumin hana zirga-zirgar da ta sanya wa matafiya ‘yan Najeriya, biyo bayan bullar kwayar cutar COVID-19 a Afirka ta Kudu da aka gano a tsakanin wasu matafiya da aka ce sun ziyarci Najeriya.
Ambasada Zubairu Dada, karamin ministan harkokin wajen kasar ne ya yi wannan roko a cikin wata sanarwa da kakakinsa Ibrahim Aliyu ya fitar, yayin da ya yaba da kyakkyawar alakar da ke tsakanin kasashen biyu tsawon shekaru.