fidelitybank

Masarautar Saudiyya ta ɗage dokar hana jiragen sama daga Najeriya da wasu ƙasashe 16

Date:

Masarautar Saudiyya ta ɗage dokar hana zirga-zirgar jiragen sama daga Najeriya da wasu kasashe 16.

Sauran kasashe sun hada da Afirka ta Kudu, Namibiya, Botswana, Zimbabwe, Lesotho, Eswatini, Mozambique, Malawi, Mauritius, Zambia, Madagascar, Angola, Seychelles, Jamhuriyyar Comoros, Habasha da Afghanistan.
Sabon tashar Lafia zai zama cibiyar watsa labarai ta Najeriya -NDPHC

Hakazalika, mahukuntan Saudiyya sun kawo karshen bayar da tazara ga jama’a a cikin masallatai biyu masu tsarki a cikin masarautar, amma sun dage da rufe hanci da baki, yayin da suke isa wurin ibada.

Hakan dai na zuwa ne a bisa wata umarni da ma’aikatar harkokin cikin gida ta Saudiyya ta fitar, kuma mai taimaka wa shugaban kasa Muhammadu Buhari kan sabbin kafafen yada labarai, Bashir Ahmad ya tabbatar a shafin Twitter.

Saudi Gazette ta ba da rahoton cewa, matafiya ba za su ƙara yin keɓewar COVID-19 na tilas ba idan sun isa Masarautar.

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta kasa (GACA) a kasar Saudiyya ta tabbatar da dakatar da zirga-zirgar jiragen sama zuwa Najeriya a wata takardar da ta aikewa dukkan kamfanonin jiragen sama da ke aiki a Saudiyya a ranar 8 ga watan Disamba, 2021.

A watan Janairun 2022, Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bukaci Saudiyya da ta dage takunkumin hana zirga-zirgar da ta sanya wa matafiya ‘yan Najeriya, biyo bayan bullar kwayar cutar COVID-19 a Afirka ta Kudu da aka gano a tsakanin wasu matafiya da aka ce sun ziyarci Najeriya.

Ambasada Zubairu Dada, karamin ministan harkokin wajen kasar ne ya yi wannan roko a cikin wata sanarwa da kakakinsa Ibrahim Aliyu ya fitar, yayin da ya yaba da kyakkyawar alakar da ke tsakanin kasashen biyu tsawon shekaru.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp