An nada tsohon dan majalisar dattawan Najeriya, Sanata Ibrahim Mohammed Ida a matsayin Wazirin Katsina.
Sarkin Yaƙin Katsina kuma sakataren masarautar Alhaji Bello Mamman Ifo ne ya tabbatar wa BBC ranar Talata.
Sanata Ida ya maye gurbin Alhaji Sani Abubakar Lugga wanda ya yi murabus daga mukamin sa na Wazirin Katsina tun a watan Fabrairu.
Sanata Ida shi ne yake rike da sarautar Sardaunan Katsina kafin nadin nasa.
An haifi Sanata Ida a birnin Katsina a shekarar 1949, kuma ya yi karatunsa na boko a Najeriya da Birataniya da kuma Amurka.
Sabon Wazirin na Katsina ya soma aikin gwamnati da Babban Bankin Najeriya, kuma ya rike mukamai da dama a gwamnati, ciki har da Babban Sakatare na Ma’aikatar Tsaron Najeriya.
Sannan ya wakilci shiyyar Katsina ta Tsakiya a majalisar dattawan kasar tsakanin 2007-2011.
Sanata Ida ya na da mata daya Hajiya Khadija da ‘ya’ya da jikoki da dama.