Masarautar Katsina da ke Arewacin Najeriya ta dakatar da sarautar Sardaunan Katsina da aka bai wa Saddiq Musa Kaita.
Wata sanarwa da Alhaji Sule Mamman Dee, Sarkin Tsaftan Katsina ya sanya wa hannu ta ce nan gaba za a tuntube shi domin yi masa karin bayani.
“Bisa ga takardar da aka ba ka ta ranar 16/4/2022 wadda aka ba ka Sarautar Sardaunan Katsina, Majalisar Mai martaba Sarkin Katsina ta umarce ni da na rubuto na sanar da kai cewa ta dakatar da Sarautar.
Komi ke nan za a tuntube ka nan gaba,” in ji sanarwar.
Tun da farko farko Sarkin Katsina ya tabbatar masa da sarautar ne a cikin wata takarda mai É—auke da sa hannunsa a ranar Asabar 16 ga watan Afrilu.
“Na amince da ba ka Sarautar Sardaunan Katsina kamar yadda ka nema,” kamar yadda Sarkin Katsina ya bayyana a cikin takardar.
Sanarwar ta ce nan gaba za a sanar da ranar bikin naÉ—in nasa.
Saddik jika ne ta bangaren uba ga sarkin Fadan Katsina Isma’ila Damale wanda shi kuma ɗa ne ga Wazirin Katsina na farko Haruna Kaita.
Haka kuma ta bangaren uwa jika ne ga Makaman Katsina Marigayi Tukur Idris Nadabo hakimin Bakori.
A kwanakin baya ne aka ba Ibrahim Ida sarautar Wazirin Katsina wanda a baya shi ne Sardaunan Katsina.
Wannan na zuwa ne bayan ajiye sarautar waziri da Alhaji Sani Lugga ya yi saboda wasu dalilai.