fidelitybank

Masarautar Katsina ta hana hawan Sallah saboda tsaro

Date:

Majalisar Masarautar Katsina ta sanar da dakatar da Durbar a lokacin bukukuwan Eid-el-Kabir a ranar Asabar.

Sanarwar dakatarwar ta fito ne a wata sanarwa da ta fitar jiya a Katsina, ta hannun mataimakin sakataren majalisar, Sule Mamman-Dee.

Ya ce, dakatarwar ta biyo bayan yanayin tsaro da ake fama da shi a jihar.

A cewar Mamman-Dee, Sarkin, Abdulmumini Kabir-Usman, ya nuna matukar damuwarsa kan matsalar tsaro a sassan masarautar, inda ya ce zai halarci Sallar Idi ne kawai a ranar Asabar.

Ya bayyana cewa, Sarkin ya shawarci al’ummar Musulmi da su ci gaba da yin addu’o’in samun zaman lafiya a jihar da kasa baki daya.

Bikin Durbar dai ya samo asali ne tun shekaru aru aru, kuma ya kunshi baje kolin fasahar hawan doki daga gundumomi da masu fada aji, wadanda suke yiwa Sarkin Mubaya’a a ranar Idi, wanda aka fi sani da ‘Hawan Daushe’ a Katsina.

A nasa bangaren, Sarkin ya jagoranci tawagar ‘yan majalisar Masarautu da hakimai da kauye a cikin jerin gwanon dawaki da aka fi sani da ‘Hawan Bariki’ domin yin mubaya’a ga gwamnan jihar, kwana guda bayan kammala Idi.

Hakazalika kakakin masarautar Daura a jihar, Usman Ibrahim ya ce majalisar ta kuma dakatar da gudanar da bukukuwan Sallah a fadin masarautar.

A cewar Ibrahim, Sarkin, Faruk Umar-Faruk ya umurci dukkanin hakimai da ke karkashin masarautar su gudanar da Sallar Idi-El Kabir a yankunansu.

Ibrahim ya ce, Sarkin ya kuma yi kira ga maniyyatan da ke zuwa aikin Hajji da su yi addu’ar zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar da kasa baki daya.

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamna Zulum ya musanta shirin sauya sheƙa zuwa ADC

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya musanta...

Tinubu ta ceci Najeriya faÉ—a wa cikin mawuyacin hali – Ribadu

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Malam...

Isra’ila za ta aika tawaga Qatar don tattaunawa da Hamas

Isra’ila ta yanke shawarar aika wata tawaga zuwa Qatar...

Jagoran Iran ya bayyana gaban jama’a karon farko tun soma yaÆ™i da Isra’ila

Jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya bayyana...

Muna aiki tukuru don bunÆ™asa noma a Najeriya – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya tabbatar da cewa...

Duk wanda ya yi sata idan na zama shugaban Æ™asa sai na yake shi – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya yi alwashin...

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke É—auka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da Æ™arfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar Æ´ansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...
X whatsapp