fidelitybank

Masarautar Katsina ta hana hawan Sallah saboda tsaro

Date:

Majalisar Masarautar Katsina ta sanar da dakatar da Durbar a lokacin bukukuwan Eid-el-Kabir a ranar Asabar.

Sanarwar dakatarwar ta fito ne a wata sanarwa da ta fitar jiya a Katsina, ta hannun mataimakin sakataren majalisar, Sule Mamman-Dee.

Ya ce, dakatarwar ta biyo bayan yanayin tsaro da ake fama da shi a jihar.

A cewar Mamman-Dee, Sarkin, Abdulmumini Kabir-Usman, ya nuna matukar damuwarsa kan matsalar tsaro a sassan masarautar, inda ya ce zai halarci Sallar Idi ne kawai a ranar Asabar.

Ya bayyana cewa, Sarkin ya shawarci al’ummar Musulmi da su ci gaba da yin addu’o’in samun zaman lafiya a jihar da kasa baki daya.

Bikin Durbar dai ya samo asali ne tun shekaru aru aru, kuma ya kunshi baje kolin fasahar hawan doki daga gundumomi da masu fada aji, wadanda suke yiwa Sarkin Mubaya’a a ranar Idi, wanda aka fi sani da ‘Hawan Daushe’ a Katsina.

A nasa bangaren, Sarkin ya jagoranci tawagar ‘yan majalisar Masarautu da hakimai da kauye a cikin jerin gwanon dawaki da aka fi sani da ‘Hawan Bariki’ domin yin mubaya’a ga gwamnan jihar, kwana guda bayan kammala Idi.

Hakazalika kakakin masarautar Daura a jihar, Usman Ibrahim ya ce majalisar ta kuma dakatar da gudanar da bukukuwan Sallah a fadin masarautar.

A cewar Ibrahim, Sarkin, Faruk Umar-Faruk ya umurci dukkanin hakimai da ke karkashin masarautar su gudanar da Sallar Idi-El Kabir a yankunansu.

Ibrahim ya ce, Sarkin ya kuma yi kira ga maniyyatan da ke zuwa aikin Hajji da su yi addu’ar zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar da kasa baki daya.

latest news in nigeria today 
2021 ripples

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp