fidelitybank

Maruba labarin wasanni su kara jajircewa a kan aikin su – Yakubu Muhammad

Date:

Shugaban kungiyar marubuta wasanni ta kasa (SWAN), reshen jihar Bauchi, Mahmud Yakubu Muhammad ya ce, kwararrun ‘yan jarida su kasance wajen bayar da rahotannin wasanni a jihar.

Ya bayar da wannan shawarar ne a ranar Litinin din da ta gabata yayin bikin bude makon SWAN na Bauchi 2022 wanda aka gudanar a cibiyar ‘yan jarida ta NUJ Bauchi.

A cewarsa, manufar makon SWAN ita ce kulla kyakkyawar alaka a tsakanin masu aikin yada labarai ta hanyar wasanni, inda ya kara da cewa, makon kuma wata hanya ce ta samar da ingantacciyar gasa ta wasanni daban-daban da za a yi a cikin mako.

Ya ce, kungiyar za ta shirya horas da marubutan wasanni a jihar domin su fadakar da su yadda ake tafiyar da harkokin wasanni tare da kara kaimi wajen bayar da rahotanni a wasanni.

Shugaban SWAN ya bayyana cewa, ya kamata ‘yan jarida su rika motsa jiki a ko da yaushe domin su kasance cikin koshin lafiya domin yana inganta lafiyar jikin mutane da kuma inganta lafiyar kwakwalwa da tunani.

“Lafiyar mambobinmu da ta sauran ‘yan jarida na da matukar muhimmanci, don haka akwai bukatar su kasance masu dacewa da hankali. Ta hanyar wasanni, za su ci gaba da kasancewa cikin koshin lafiya, ta yadda za su yi aiki mafi kyau a ayyukansu a matsayin masu aikin watsa labarai, ”in ji shi

Shima da yake jawabi, shugaban kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ), majalisar jihar Bauchi, Kwamared Umar Sa’idu, ya ce wasanni ba wasa ba ne na nishadantarwa ko kasuwanci, illa dai karfi ne da ke hada kan ‘yan Najeriya.

Ya yabawa kungiyoyin yada labarai na jihar kan yadda suke bunkasa harkokin wasanni ta hanyar rahotannin da suke bayarwa tare da karfafa musu gwiwa su ci gaba da gudanar da ayyukansu.

www.legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp