fidelitybank

Marigayi Ado Bayero ya ce ni ne zan zama shugaban kasa – Atiku

Date:

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya tunatar da mai martaba Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero cewa mahaifinsa, Alhaji Ado Bayero, ya shaida musu a wata ziyara da ya kai fadar cewa shi (Atiku) zai zama shugaban kasa.

“Mun kai ziyarar ban girma zuwa fadar a wani lokaci a lokacin da nake Mataimakin Shugaban Najeriya, sai marigayi Sarki Ado Bayero ya ce a cikinmu ya ga wani da zai zama Shugaban kasa wanda zai kawo wa Najeriya girma.” Inji Atiku.

Atiku Abubakar ya kara da cewa marigayi sarki Ado Bayero bai tsaya a haka ba. Ya kuma ci gaba da addu’ar Allah ya baiwa shugaban kasar da ya gani ya kawo wa Nijeriya hayyacinta, ya kuma inganta zamantakewa da tattalin arzikinta.

Karanta Wannan: Kotu ta hana Wike kama magoya bayan Atiku

Ya ce, ya yi imanin cewa shi ne wanda Marigayi Sarki Ado Bayero ya ambata shi ya sa ya zama wajibi mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya yi koyi da shi tare da yi masa addu’a domin cimma burin Marigayi Bayero.

Atiku Abubakar, wanda ke Kano a kan yakin neman zabensa na shugaban kasa, ya kasance a fadar sarkin kasar a ziyarar ban girma, tare da mukarrabansa, ciki har da dan takarar mataimakinsa Ifeanyi Okowa.

labaran duniya na yau

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar ƴan Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya zai tattauna yau...

Sojoji sun kashe ‘yan Boko Haram 17 a Borno da Adamawa

Sojoji da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Haɗin Kai...

Falana ya caccaki Tinubu kan salon tattalin arzikin Najeriya

Fitaccen lauyan nan mai kare haƙƙin bil adama, Femi...

Yahudawa sun yiwa Netanyahu tutsu kan mamaye Gaza

Ƴan'uwan Isra'ilawan da aka yi garkuwa da su a...

Cin zarafin Daliba ya sanya yin zanga-zanga a China

Zanga-zanga ta ɓarke a kudancin China sakamakon cin zarafin...

Tinubu ya baiwa ‘yan wasan kwallon kwando dala dubu 100 da filaye a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta karrama kungiyar kwallon kwando ta mata...

‘Yan siyasa na kara matsin lamba Jonathan ya fito takara a 2027 – Bashir

Tsohon mai taimaka wa tsohon shugaban kasa kan harkokin...

Gwamnati ta karbi tawagar ‘yan wasan kwallon kwando D’Tigress

Tawagar ƴan wasan ƙwallon kwando mata ta Najeriya ta...
X whatsapp