fidelitybank

Manyan Ɓarayin mai a Legas da Abuja su na son kashe ni – Tampolo

Date:

Mai kamfanin Tantita Security Services Nigeria Limited, Government Ekpemupolo, wanda aka fi sani da Tompolo, ya yi ikirarin cewa manyan barayin mai a jihar Legas da Abuja, babban birnin tarayya, suna son kashe shi.

Tompolo ya bayyana hakan ne a kwanan baya yayin wata ziyarar aiki da kungiyar lauyoyin Najeriya ta kasa karkashin jagorancin shugabanta Afam Osigwe (SAN) suka kai wa Oporoza hedkwatar masarautar Gbaramatu.

Ya yi zargin cewa masu karfi da ke wajen yankin Neja Delta ne ke bayan barayin mai a yankin.

A cewarsa, ya taka yatsu da yawa yayin da yake gudanar da aikinsa na kare bututun mai a yankin Neja Delta.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Tompollo ya yi kira da a hada kai tsakanin sojojin ruwa da sauran jami’an tsaro domin kara sanya ido kan bututun danyen mai na kasar a yankin Neja Delta.

“A yayin da muke wannan aikin, mun taka kafar mutane da yawa a can Legas da Abuja. Mun taka yatsu da yawa.

“Yayin da nake nan, bayan shari’ar da nake yi a kotu, ba zan iya tafiya ko’ina ba saboda ni da manyan mutane (baron) da suke yakar wannan yakin.

“Idan ina son tafiya Abuja in ziyarce ku, dole ne in tafi da jami’an tsaro. Ko da jami’an tsaro biyu ko uku, babu wanda ya yi farin ciki da ni a cikinsu, kuma a yanzu suna hada kai da manyan ‘yan wasa masu satar mai,” inji shi.

tribune news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp