Shugabannin siyasa na Taiwan haɗi da Shugabar kasar, Tsai Ing-wen, za su bayar da albashinsu na wata daya, domin tallafa wa mutanen da suke tserewa daga yakin Ukraine.
Mataimakin shugabar kasar da firimiya da kuma shugabannin ‘yan hamayya na daga cikin wadanda suka yi alkawarin ba da albashinsu.
Shugaba Tsai ta ce tana fatan dukkanin alummar Taiwan da ma’aikatan gwamnati za su taimaka wa al’ummar ta Ukraine.
Ta ce: ”Ma’aikatar Harkokin Waje za ta sanar da kafa asusun banki na musamman domin tattara tallafin na Ukraine, wanda hukumar ba da tallafin gaggawa ta samar. Hatta daidaikun jama’ar kasar ta Taiwan an bukace su da su ba da tallafin.”
Bayan tallafin kudi da za ta bayar, gwamnatin Japan tana kuma shirin aikawa da taimakon kayayyakin kula da lafiya domin ‘yan gudun hijirar na Ukraine.
Taiwan na nuna goyon bayanta ga Ukraine, saboda ita ma tana fuskantar irin wannan barazana ta mamaya daga China, wadda ke ikirarin tsibirin nata ne. In ji BBC.