fidelitybank

Manyan ‘yan siyasa da shugaban kasar Taiwan za su bayar da albashin su ga Ukraine

Date:

Shugabannin siyasa na Taiwan haɗi da Shugabar kasar, Tsai Ing-wen, za su bayar da albashinsu na wata daya, domin tallafa wa mutanen da suke tserewa daga yakin Ukraine.

Mataimakin shugabar kasar da firimiya da kuma shugabannin ‘yan hamayya na daga cikin wadanda suka yi alkawarin ba da albashinsu.

Shugaba Tsai ta ce tana fatan dukkanin alummar Taiwan da ma’aikatan gwamnati za su taimaka wa al’ummar ta Ukraine.

Ta ce: ”Ma’aikatar Harkokin Waje za ta sanar da kafa asusun banki na musamman domin tattara tallafin na Ukraine, wanda hukumar ba da tallafin gaggawa ta samar. Hatta daidaikun jama’ar kasar ta Taiwan an bukace su da su ba da tallafin.”

Bayan tallafin kudi da za ta bayar, gwamnatin Japan tana kuma shirin aikawa da taimakon kayayyakin kula da lafiya domin ‘yan gudun hijirar na Ukraine.

Taiwan na nuna goyon bayanta ga Ukraine, saboda ita ma tana fuskantar irin wannan barazana ta mamaya daga China, wadda ke ikirarin tsibirin nata ne. In ji BBC.

vgn news 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp