Kocin Super Eagles, Jose Peseiro, ya bayyana dalilan da yasa manyan kungiyoyi kamar Chelsea, Manchester United, Real Madrid da Tottenham Hotspur ke zawarcin Victor Osimhen.
Osimhen ya zama abin labari, saboda bajintar da ya ci tun lokacin da ya koma Napoli daga kulob din Lille 1 a 2020.
A kakar wasa ta bana, dan wasan mai shekaru 23 ya zura kwallaye tara a wasanni 13 da ya buga a Napoli.
A halin yanzu Osimhen yana daya daga cikin ‘yan wasan gaba da ake nema ruwa a jallo a duniya a halin yanzu.
Peseiro ya bayyana cewa babu wata kungiya a duniya da zata wuce daman samun Osimhen a kungiyar saboda halayensa.
“Yana zura kwallaye da yawa kuma matashi ne. Tabbas ba abu ne mai sauki ba, yawanci dan wasan gaba yana samun wannan matakin daga baya,” Peseiro ya fada wa gidan yanar gizon Italiyanci, Tuttomercatoweb.
“Amma yakan zira kwallaye a raga, a wannan lokacin, bana jin banyi kuskure ba idan nace kowace kungiya a duniya tana son siyan shi.
“Ya san yadda ake dannawa, ya san yadda ake zura kwallo, ya san yadda ake amfani da jikinsa. Zai san yadda ake buga wasa a dukkan kungiyoyi.”
Ana sa ran za a saka sunan Osimhen a cikin ‘yan wasan Najeriya da za su buga wasan sada zumunta da Portugal.