fidelitybank

Manyan kungiyoyi na zawarcin Osimhen – Mai horas da Najeriya

Date:

Kocin Super Eagles, Jose Peseiro, ya bayyana dalilan da yasa manyan kungiyoyi kamar Chelsea, Manchester United, Real Madrid da Tottenham Hotspur ke zawarcin Victor Osimhen.

Osimhen ya zama abin labari, saboda bajintar da ya ci tun lokacin da ya koma Napoli daga kulob din Lille 1 a 2020.

A kakar wasa ta bana, dan wasan mai shekaru 23 ya zura kwallaye tara a wasanni 13 da ya buga a Napoli.

A halin yanzu Osimhen yana daya daga cikin ‘yan wasan gaba da ake nema ruwa a jallo a duniya a halin yanzu.

Peseiro ya bayyana cewa babu wata kungiya a duniya da zata wuce daman samun Osimhen a kungiyar saboda halayensa.

“Yana zura kwallaye da yawa kuma matashi ne. Tabbas ba abu ne mai sauki ba, yawanci dan wasan gaba yana samun wannan matakin daga baya,” Peseiro ya fada wa gidan yanar gizon Italiyanci, Tuttomercatoweb.

“Amma yakan zira kwallaye a raga, a wannan lokacin, bana jin banyi kuskure ba idan nace kowace kungiya a duniya tana son siyan shi.

“Ya san yadda ake dannawa, ya san yadda ake zura kwallo, ya san yadda ake amfani da jikinsa. Zai san yadda ake buga wasa a dukkan kungiyoyi.”

Ana sa ran za a saka sunan Osimhen a cikin ‘yan wasan Najeriya da za su buga wasan sada zumunta da Portugal.

mmm.nnn.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Æ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maÆ™ale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin Æ´an Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taÉ“a barin Iran ta Æ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp