fidelitybank

Manyan dalilan da ya sanya INEC za ta takawa Peter Obi birki – Tsohon Hadimin Buhari

Date:

Bashir Ahmad, wanda tsohon hadimin shugaban kasa, Muhammadu Buhari ne, ya bayar da wani dalilin da zai sa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta soke Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party, LP.

Idan dai ba a manta ba a jiya ne jam’iyyar PDP ta yi irin wannan kiran, inda ta ce, an yi musanya da abokin takarar ta ba bisa ka’ida ba.

PDP ta bukaci kotun da ta kori Obi da dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress, APC, saboda amfani da masu rike da mukamai, daga bisani kuma suka sanar da sabbin abokan takara.

Hakazalika, Ahmad ya nuna cewa, bai kamata Obi ya tsaya takarar shugabancin kasa a karkashin jam’iyyar Labour ba, wanda ya shiga a watan Mayun 2022.

Ku tuna cewa kafin zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Peter ya fice daga babbar jam’iyyar adawa ya koma jam’iyyar LP, inda ya tsaya takarar zaben fidda gwani kuma ya yi nasara.

Ahmad ya yi ikirarin cewa, sunan Obi baya cikin jerin sunayen mambobin LP da jam’iyyar ta mika wa INEC.

“A daidai da EA2022, ya kamata INEC ta hana dan takarar shugaban kasa na LP tsayawa takara a zaben 2023.

“Dan takarar ba ya cikin jerin sunayen mambobin jam’iyyar da aka mika wa hukumar zabe. An gabatar da jerin sunayen ne a ranar 25 ga Afrilu, yayin da dan takarar ya koma jam’iyyar a ranar 26 ga Mayu,” ya wallafa a shafinsa na Twitter.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp