fidelitybank

Manyan dalilan da ya sanya INEC za ta takawa Peter Obi birki – Tsohon Hadimin Buhari

Date:

Bashir Ahmad, wanda tsohon hadimin shugaban kasa, Muhammadu Buhari ne, ya bayar da wani dalilin da zai sa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta soke Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party, LP.

Idan dai ba a manta ba a jiya ne jam’iyyar PDP ta yi irin wannan kiran, inda ta ce, an yi musanya da abokin takarar ta ba bisa ka’ida ba.

PDP ta bukaci kotun da ta kori Obi da dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress, APC, saboda amfani da masu rike da mukamai, daga bisani kuma suka sanar da sabbin abokan takara.

Hakazalika, Ahmad ya nuna cewa, bai kamata Obi ya tsaya takarar shugabancin kasa a karkashin jam’iyyar Labour ba, wanda ya shiga a watan Mayun 2022.

Ku tuna cewa kafin zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Peter ya fice daga babbar jam’iyyar adawa ya koma jam’iyyar LP, inda ya tsaya takarar zaben fidda gwani kuma ya yi nasara.

Ahmad ya yi ikirarin cewa, sunan Obi baya cikin jerin sunayen mambobin LP da jam’iyyar ta mika wa INEC.

“A daidai da EA2022, ya kamata INEC ta hana dan takarar shugaban kasa na LP tsayawa takara a zaben 2023.

“Dan takarar ba ya cikin jerin sunayen mambobin jam’iyyar da aka mika wa hukumar zabe. An gabatar da jerin sunayen ne a ranar 25 ga Afrilu, yayin da dan takarar ya koma jam’iyyar a ranar 26 ga Mayu,” ya wallafa a shafinsa na Twitter.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

JAMB ta amince da maki 150 mafi ƙanƙanta don samun gurbin karatu a jami’o’i

Hukumar shirya jarrabawar shiga Jami'o'i ta Najeriya (JAMB) ta...

ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Najeriya, ASUU da dakatar yajin...

Masu haɗakar ADC na ɓaɓatu ne saboda rashin gwamnati – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umar Radda ya yi...

Ba ruwan Biri da gada a makamin Nukiliya – Shettima

Mataimakin shugaba Najeriya Kashim Shettima ya ce ƙasar za...

An kashe Mutane 70 a jihar Filato

Rahotonni daga jihar Filato na cewa ƴanbindiga sun kai...

Ambaliya ta kashe mutane 100 a Amurka

Hukumomi a jihar Tesxas da ke Amurka sun bayyana...

Tsohon Ministan kuma jigo a PDP ya koma ADC

Tsohon ministan harkokin ‘yan sanda kuma sau uku a...

Trump ya caccaki Elon Musk

Shugaban Amurka Donald Trump ya caccaki tsohon mashawarcinsa, Elon...

Dalilin da ya sa Kwankwaso ya ki shiga jam’iyyar hadaka – Galadima

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...

Obi ba zai taba zama shugaban kasa ba – Wike

Ministan Abuja, Nyesom Wike ya ce, tsohon ɗan takarar...

Ƴansanda sun kama ƴan Ghana 19 da aka yi safararsu a Najeriya

Rundunar ƴansandan Najeriya ta kuɓutar da wasu ƴan Ghana...

Benue da Edo da Bayelsa na fargabar balewar madatsar ruwan Kamaru

Gwamnatocin jihohi uku na cikin shirin ko-ta -kwana, sakamakon...
X whatsapp