fidelitybank

Manoman Borno sun fara addu’ar roƙon ruwa

Date:

Manoman jihar Borno sun gudanar da addu’o’i na musamman, saboda rashin samun ruwan sama.

Kamfanin Dillancin Labarai na ƙasa NAN ya ruwaito cewa, manoman da galibinsu a yankunan arewaci da tsakiyar jihar da ci gaban ya shafa sun koma yin addu’o’in neman taimakon Allah.

Manoman da dama a kananan hukumomin Maiduguri, Jere, Konduga, Kaga da Mafa sun ce ci gaban ya tayar da hankali kuma suna bukatar addu’a.

“Za ku ga gajimare kamar za a yi ruwan sama amma bayan wani lokaci za a yi iska mai ƙarfi tana tura gajimaren zuwa wani wuri kuma ƙarshen ke nan.

“Idan abubuwa suka ci gaba da tafiya haka za a samu fari,” wani manomi a wajen birnin Maiduguri, Malam Ibrahim Ali, ya shaida wa NAN.

Manoman da dama da su ma suka yi magana kan wannan lamari mai tada hankali, sun ce sun koma yin addu’a.

A halin da ake ciki, Majalisar Masarautar Borno ta fara jan hankalin jama’a domin gudanar da addu’o’in samun ruwan sama, wanda ake kira “Salatul Istisqa’a”.

Sanarwa daga Shehun Borno, Alhaji Abubakar Umar Garbai El-Kanemi, ya bukaci al’ummar Musulmi da su hallara a dandalin Ramat Square Maiduguri a yau Litinin domin yin addu’a.

Sanarwar mai dauke da sa hannun sakataren Shehu Malam Zannah-Umar Ali, ta bukaci al’ummar musulmi da su tashi tsaye ba tare da la’akari da shekaru, jinsi da matsayi domin gudanar da addu’a ta musamman ba.

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp