fidelitybank

Manoma da ‘yan Banga za su kare Manoma a gonakin su – Gwamnatin Yobe

Date:

Gwamnatin jihar Yobe ta dauki nauyin sojojin da ’yan banga don kare manoma da amfanin gonakinsu a jihar.

Manoma a kananan hukumomin Gujba, Damaturu, Karasuwa, da Gashua suna gama da sintirin sanya idanu akan gonakinsu domin kula da amfanin gonakinsu a wannan kakar daga fadawa hannun ‘yan ta’adda.

Da yake jawabi ga manema labarai bayan taron tsaro na jihar wanda mataimakin gwamnan ya jagoranta, mai baiwa gwamna shawara na musamman kan harkokin tsaro, Birgediya Janar Abdulsalam Dahiru (Rtd) ya ce gwamnatin jihar ta dauki matakin shawo kan matsalar.

Ya ce gwamnatin jihar ta yanke shawarar hada sojoji da ’yan banga don kare amfanin gona daga batagarin musamman la’akari da yanda matsalar tsaro ta ta’azzara a yankin.

Dahiru ya ce an samar da babura 70 don amfanin jami’an soji da kungiyoyin mafarauta da ’yan banga da ke sintiri a daukacin yankunan da abin ya shafa domin kare amfanin gona da manoma daga barayi da ‘yan ta’adda.

Ya ce an kwashe watanni uku ana gudanar da wannan aiki kuma za a ci gaba da gudanar da aikin har zuwa watan Janairun shekarar 2025 inda manoma za su kwashe dukkan amfanin gonakin da aka girbe.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp