fidelitybank

Manoma da ‘yan Banga za su kare Manoma a gonakin su – Gwamnatin Yobe

Date:

Gwamnatin jihar Yobe ta dauki nauyin sojojin da ’yan banga don kare manoma da amfanin gonakinsu a jihar.

Manoma a kananan hukumomin Gujba, Damaturu, Karasuwa, da Gashua suna gama da sintirin sanya idanu akan gonakinsu domin kula da amfanin gonakinsu a wannan kakar daga fadawa hannun ‘yan ta’adda.

Da yake jawabi ga manema labarai bayan taron tsaro na jihar wanda mataimakin gwamnan ya jagoranta, mai baiwa gwamna shawara na musamman kan harkokin tsaro, Birgediya Janar Abdulsalam Dahiru (Rtd) ya ce gwamnatin jihar ta dauki matakin shawo kan matsalar.

Ya ce gwamnatin jihar ta yanke shawarar hada sojoji da ’yan banga don kare amfanin gona daga batagarin musamman la’akari da yanda matsalar tsaro ta ta’azzara a yankin.

Dahiru ya ce an samar da babura 70 don amfanin jami’an soji da kungiyoyin mafarauta da ’yan banga da ke sintiri a daukacin yankunan da abin ya shafa domin kare amfanin gona da manoma daga barayi da ‘yan ta’adda.

Ya ce an kwashe watanni uku ana gudanar da wannan aiki kuma za a ci gaba da gudanar da aikin har zuwa watan Janairun shekarar 2025 inda manoma za su kwashe dukkan amfanin gonakin da aka girbe.

vanguard 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...
X whatsapp