fidelitybank

Maniyatan Kano sun yi zanga-zanga akan ta leƙo ta koma da aka yi musu

Date:

Wasu daga cikin maniyata aikin hajjin jihar Kano sama da dari 300 sun zargi hukumar jindadin alhazan jihar da yi musu ta leko ta koma kan tafiyarsu aikin hajjin bana.

Minyatan dai sun ce sun biya kudaden su na tafiya fiye da shekara guda, sannan har an gama tantance su, sai daga bisani bayan alhazan Kanon sun fara tafiya aka zo aka sanar da su cewa babu su a aikin hajjin na bana.

Maniyittan da suka yiwa ofishin alhazai na Kano tsinke sun ce ba za su amince da wannan tsarin na tauye mu su hakki ba.

Wata dattijuwa da ta fito daga Karamar hukumar Dawakin kudu ta ce sai da ta gama dukkan shirin tafiya har ma ta karbi jaka aka ce mata ta dawo

Abba Dambatta shine shugaban hukumar alhazai ta jihar Kano, ya ce babu hannun hukumarsa a wajen matsalar da suka fuskanta, don babu wanda ya saka kudin asusun da suka bayar

Sai dai duk kokarin da BBC ta yi don jin ta bakin ofishin hukumar ralhazai na Najeriya hakan ya ci tura, sakamakon rashin amsa kira wayar da dawo da amsar sakon da mu ka aikewa jami’ar hulda da jama’a na hukumar Hajiya Fatima Sanda Usara.

Wannan dai na zuwa ne kwana guda da fara tashin alhazan jihar Kano, wanda kimanin alhazai sama da dubu biyu ake sa ran za su isa kasa mai tsarki don yin aikin hajjin bana.

Ko a makonin da suka gabata sai da aka sami musayar kalamai tsakanin hukumar jin dadin alhazai a Kano da Kamfanin jirgin sama na Azman kan jigilar alhazan jihar da aka ce kamfanin zai yi tare da jirgin Max Air da Fly Nas mallakar kasar Saudiya.

vanguard news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

JAMB ta amince da maki 150 mafi ƙanƙanta don samun gurbin karatu a jami’o’i

Hukumar shirya jarrabawar shiga Jami'o'i ta Najeriya (JAMB) ta...

ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Najeriya, ASUU da dakatar yajin...

Masu haɗakar ADC na ɓaɓatu ne saboda rashin gwamnati – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umar Radda ya yi...

Ba ruwan Biri da gada a makamin Nukiliya – Shettima

Mataimakin shugaba Najeriya Kashim Shettima ya ce ƙasar za...

An kashe Mutane 70 a jihar Filato

Rahotonni daga jihar Filato na cewa ƴanbindiga sun kai...

Ambaliya ta kashe mutane 100 a Amurka

Hukumomi a jihar Tesxas da ke Amurka sun bayyana...

Tsohon Ministan kuma jigo a PDP ya koma ADC

Tsohon ministan harkokin ‘yan sanda kuma sau uku a...

Trump ya caccaki Elon Musk

Shugaban Amurka Donald Trump ya caccaki tsohon mashawarcinsa, Elon...

Dalilin da ya sa Kwankwaso ya ki shiga jam’iyyar hadaka – Galadima

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...

Obi ba zai taba zama shugaban kasa ba – Wike

Ministan Abuja, Nyesom Wike ya ce, tsohon ɗan takarar...

Ƴansanda sun kama ƴan Ghana 19 da aka yi safararsu a Najeriya

Rundunar ƴansandan Najeriya ta kuɓutar da wasu ƴan Ghana...

Benue da Edo da Bayelsa na fargabar balewar madatsar ruwan Kamaru

Gwamnatocin jihohi uku na cikin shirin ko-ta -kwana, sakamakon...
X whatsapp