A yau Litinin ne rukunin farko na alhazan jihar Kano daga arewacin Najeriya suka tashi zuwa Saudiyya don gudanar da aikin Hajjin bana.
Gwamna Abba Kabir Yusuf da mataimakinsa Aminu Abdussalam ne suka yi wa alhazan rakiya zuwa filin jirgi, inda gwamnan ya nemi su kiyaye dokokin ƙasar yayin zaman ibadar da suka je yi.
Rahotonni na cewa alhazai 550 ne suka tashi daga filin jirgin sama na Mallam Aminu Kano da ke jihar.