Maniyatan jihar Nasarawa sun yi hatsari a kan hanyar su ta zuwa Abuja.
Hatsarin mota ya ritsa da wasu maniyyata daga Jihar Nasarawa a yau Laraba.
Lamarin ya faru ne yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa Abuja babban birnin ƙasar, kamar yadda wani mai magana da yawun hukumar aikin Hajji a Najeriya ya tabbatar wa BBC.
Babu wanda ya rasa ransa a hatsarin yayin da motar bas ɗin da suke ciki ta hantsila a kusa da garin Keffi mai maƙwabtaka da Abuja.
Sai dai babu tabbas game da yawan waɗanda suka ji raunuka.
A gobe Alhamis ne ake sa ran fara kwashe maniyyata aikin Hajjin na bana zuwa Saudiyya daga filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe da ke Abuja.