fidelitybank

Maniyatan jihar Legas na farko sun ta shi zuwa Saudiyya

Date:

Gwamnatin jihar Legas ta tabbatar da tashin kashin farko na maniyyata 388 da za su yi aikin Hajjin shekarar 2024 zuwa kasar Saudiyya.

A cewar sanarwar da aka fitar ranar Talata, alhazan sun tashi daga tashar jirgin saman Murtala Muhammed da ke Ikeja da misalin karfe 5:42 na rana. ran Litinin.

Sun yi tafiya ne a cikin jirgin FLYNAS Airbus A330-300 mai lamba XY8410. Kungiyar ta kunshi alhazai 167 maza da mata 221.

Kwamishinan harkokin cikin gida, Hon. Ibrahim Layode tare da wasu manyan jami’an gwamnati sun halarci filin jirgin domin ganin maniyyatan. A nasa jawabin, Layode ya bukaci maniyyatan da su ci gaba da mai da hankali kan ruhi da kuma tabbatar da cikakken aiki da ayyukan Hajji kamar yadda Manzon Allah (SAW) ya tsara.

Ya jaddada kudirin Gwamna Babajide Sanwo-Olu na jin dadin alhazai, inda ya bada misali da shirye-shiryen tallafi na baya-bayan nan, ciki har da duban lafiya da yawa da aka gudanar a wurare 10 na jihar domin tabbatar da shirinsu na zuwa aikin hajji.

Layode ya kuma shawarci mahajjatan da su kasance cikin tarbiya da gaskiya, inda ya bukace su da su zama wakilai nagari na jihar Legas da Najeriya ta hanyar bin doka da al’adun Saudiyya.

Shi ma babban sakataren hukumar jin dadin alhazai ta jihar Legas, AbdulHakeem Ajomagberin, ya yi jawabi ga kungiyar, inda ya ja kunnen su da su guji duk wani hali da ka iya kawo bata sunan jihar ko kasa.

Ajomagberin ya bayyana cewa za a ci gaba da jigilar maniyyatan da za su biyo baya kamar yadda hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta tsara, inda za a ci gaba da jigilar maniyyata a ranar Talata.

Ya kara da cewa za a dakatar da ayyukan ne a ranar Laraba kuma za a ci gaba da aiki daga ranar Alhamis zuwa Asabar, inda jirgin na ranar Asabar ya kammala atisayen jigilar jirage na Legas.

sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp