Gwamnatin jihar Legas ta tabbatar da tashin kashin farko na maniyyata 388 da za su yi aikin Hajjin shekarar 2024 zuwa kasar Saudiyya.
A cewar sanarwar da aka fitar ranar Talata, alhazan sun tashi daga tashar jirgin saman Murtala Muhammed da ke Ikeja da misalin karfe 5:42 na rana. ran Litinin.
Sun yi tafiya ne a cikin jirgin FLYNAS Airbus A330-300 mai lamba XY8410. Kungiyar ta kunshi alhazai 167 maza da mata 221.
Kwamishinan harkokin cikin gida, Hon. Ibrahim Layode tare da wasu manyan jami’an gwamnati sun halarci filin jirgin domin ganin maniyyatan. A nasa jawabin, Layode ya bukaci maniyyatan da su ci gaba da mai da hankali kan ruhi da kuma tabbatar da cikakken aiki da ayyukan Hajji kamar yadda Manzon Allah (SAW) ya tsara.
Ya jaddada kudirin Gwamna Babajide Sanwo-Olu na jin dadin alhazai, inda ya bada misali da shirye-shiryen tallafi na baya-bayan nan, ciki har da duban lafiya da yawa da aka gudanar a wurare 10 na jihar domin tabbatar da shirinsu na zuwa aikin hajji.
Layode ya kuma shawarci mahajjatan da su kasance cikin tarbiya da gaskiya, inda ya bukace su da su zama wakilai nagari na jihar Legas da Najeriya ta hanyar bin doka da al’adun Saudiyya.
Shi ma babban sakataren hukumar jin dadin alhazai ta jihar Legas, AbdulHakeem Ajomagberin, ya yi jawabi ga kungiyar, inda ya ja kunnen su da su guji duk wani hali da ka iya kawo bata sunan jihar ko kasa.
Ajomagberin ya bayyana cewa za a ci gaba da jigilar maniyyatan da za su biyo baya kamar yadda hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta tsara, inda za a ci gaba da jigilar maniyyata a ranar Talata.
Ya kara da cewa za a dakatar da ayyukan ne a ranar Laraba kuma za a ci gaba da aiki daga ranar Alhamis zuwa Asabar, inda jirgin na ranar Asabar ya kammala atisayen jigilar jirage na Legas.