Hukumar Alhazai ta kasa NAHCON, ta tabbatar da rasuwar Hasiya Aminu, wata maniyaciyar jihar Kaduna.
Ta rasu ne a cikin barcin da take yi jim kadan, bayan ta dawo daga dutsen Arafat, kamar yadda makwabtanta a cikin tanti suka bayyana.
Dakta Usman Galadima, babban jami’in aiyuka, kuma shugaban ma’aikatan lafiya na kasa, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) cewa, har yanzu ba a tantance dalilin mutuwar ta ba.
Ya ce, tuni aka sanar da iyalan ta rasuwarta kuma za a yi jana’izarta kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.
Usman shi ne mahajjaci na biyu da ya rasu a aikin Hajjin 2022.
Hajiya Aisha Ahmed daga Keffi a jihar Nasarawa ita ma ta rasu a makon jiya bayan gajeriyar rashin lafiya kuma an yi jana’izarta a Makkah.
Zaman Arafa a tsawon yini ya zama wajibi ga kowane mahajjaci ya cika domin yin aikin Hajji.
Alhazan Najeriya daga cikin sama da miliyan daya da ke aikin Hajjin shekarar 2022 a Arafat.
Arafat ita ce wurin da Annabi Muhammad ya gabatar da hudubarsa ta karshe a ranar Juma’a kafin rasuwarsa.