Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an tabbatar da rasuwarsa a birnin Makkah na kasar Saudiyya, sa’o’i 24 kacal da fara gudanar da ayyukan Hajji na shekarar 2025.
Kakakin Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Malam Suleiman Dederi, ya tabbatar da haka, inda ya bayyana cewa Jibrin ya rasu ne a ranar Talata bayan ya yi fama da rashin lafiya.
Daya daga cikin ‘yan uwan mamacin mai suna Sama’uddin Aliyu Kadawa, wanda ke aikin hajji, shi ma ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a Makkah.
“Lafiya kuwa ya bar gida, bayan ya yi rashin lafiya, ya kwantar da shi a Asibitin Sarki Abdulazeez na tsawon kwanaki biyu kuma an sallame shi bayan da lafiyarsa ta samu sauki.
Ya kara da cewa, “Abin takaici, lafiyarsa ta sake tsananta a jiya, inda aka garzaya da shi asibiti, duk da kokarin da likitocinmu na Najeriya da ma’aikatan lafiya suka yi a asibitin, ya rasu da misalin karfe 2:50 na safe.” Ya kara da cewa.
Aliyu ya bayyana cewa dan uwansa wanda yanzu marigayi Jibrin ya kasance manomi ne a garin Gargai da ke karamar hukumar Bebeji ta jihar Kano. Ya kuma bayyana cewa mutumin yana da tarihin ciwon ulcer da hawan jini amma likitocin asibitin Saudiyya sun bayyana cewa ya kamu da ciwon zuciya da bugun zuciya wanda hakan ya yi sanadiyar mutuwarsa.