fidelitybank

Maniyaccin jihar Legas ya rasu a Saudiyya

Date:

Jihar Legas ta rasa daya daga cikin maniyyacin ta aikin hajjin bana a kasar Saudiyya.

Marigayin mai suna Oloshogbo Isiaka Idris, ya rasu ne bayan ya dawo daga dawafi a Makkah.

A cewar wata sanarwa da mataimakin daraktan hulda da jama’a na hukumar jin dadin alhazai ta jihar Legas, Taofeek Lawal, sakataren hukumar Saheed Onipede ya fitar a ranar Laraba, ya bayyana cewa, marigayin mai shekaru 68 ya fito ne daga karamar hukumar Shomolu ta jihar.

Ya kuma rasu yana cin abincinsa bayan sallar isha’i.

Ko da yake ya ce, har yanzu ba a gano musabbabin mutuwar Idris a likitance ba, amma ba za a iya rasa nasaba da cutar hawan jinni ba.

Ya kara da cewa, an yi jana’izar marigayi Idris a Makkah bisa ka’idojin hukumomin Saudiyya, yayin da wani ma’aikacin hukumar Waheed Ololade Shonibare ya jagoranci wasu jami’an gwamnatin jihar da wasu alhazai wajen gudanar da sallar janaza ga mahajjata a Kabah.

Yayin da yake mika ta’aziyyar gwamnatin jihar ga ‘yan uwa da abokan arziki na marigayin, ya yi addu’ar A… ya gafarta masa kurakuransa, ya kuma ba shi Aljanat Fridaos da kuma ladan aikin Hajji.

Sakataren hukumar ya kuma yi kira ga sauran maniyatan da su yi taka-tsan-tsan tare da kiyaye wuce gona da iri kafin a fara aikin hajji na bana.

 

vgn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp