Rahotanni daga kasar Ingila sun bayyana cewa, kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ta tsayar da ranar Kirsimeti ga Pep Guardiola domin yanke shawara kan makomarsa a kungiyar ta Premier.
Kwantiraginsa na yanzu zai kare a lokacin rani na 2025.
A cewar Sky Sports, zakarun Ingila ba sa son shiga sabuwar shekara tare da rashin tabbas game da makomar Guardiola.
Za su bukaci Guardiola ya sanar da kulob din matakin da ya dauka a lokacin Kirsimeti domin a fara neman wanda zai maye gurbinsa, idan har ya yanke shawarar kin sanya hannu kan wata sabuwar yarjejeniya.
Mai horas War mai shekaru 53 a duniya ya shafe shekaru takwas a City, tsawon lokacin da ya shafe a kowace kungiya.
A farkon wannan bazarar, Guardiola ya nuna cewa, zai iya barin kungiyar nan ba da jimawa ba, kamar yadda ya bayyana karara cewa, ya kusa barin Etihad fiye da zama.