fidelitybank

Manchester City ce kadai da ta ci wasa uku a jere

Date:

Sheffield United ta yi rashin nasara da ci 2-1 a gida a hannun Manchester City a wasan mako na uku a Premier League ranar Lahadi.

Kungiyoyin biyu sun kammala zagayen farko ba tare da cin kwallo a raga ba.

Bayan da suka koma zagaye na biyu ne Erling Haaland ya ci kwallon farko, amma kuma Jayden Bogle ya farke, saura minti biyar a tashi wasan.

To sai dai City ta samu maki ukun da take buƙata bayan da Rodrigo Hernandez ya zura na biyu a raga, saura minti biyu lokaci ya cika.

City ta buga karawar ba tare da kociyanta Pep Guardiola ba, wanda aka yi masa aiki da ba zai ja ragamar karawa biyu ba a jere.

Ranar 2 ga watan Satumba, City za ta karbi bakuncin Fulham a karawar mako na hudu a Premier League.

Kungiyar da ke Etihad ta fara da cin Burnley 3-0 ranar 12 ga watan Agusta da fara kakar bana, sannan ta yi nasara a kan Newcastle United da ci 1-0 ranar 19 ga watan Agusta.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp