fidelitybank

Manajan Binance ya tsere daga Najeriya

Date:

Ofishin masu ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, ONSA, ya tabbatar da tserewar Manajan Binance na Afirka, Nadeem Anjarwalla.

Rahotanni na cewa Anjarwalla, Manaja na yankin Afirka na Binance, ya tsere daga tsare a ranar 22 ga Maris, 2024, daga wani masaukin baki na Abuja, inda aka tsare shi da abokin aikinsa, Tigran Gambaryan bisa zargin kin biyan haraji.

Wata sanarwa da shugaban sashen yada labarai na ONSA, Zakari Mijinyawa ya fitar, ta ce Anjarwalla ya tsere daga Najeriya ta hanyar amfani da fasfo na bogi.

Mijinyawa ya ce an kama jami’an da ke da alhakin tsare wanda ake zargin kuma an fara bincike.
“Bincike na farko ya nuna cewa Mista Anjarwalla ya tsere daga Najeriya ta hanyar amfani da fasfo na bogi”.

Sanarwar ta ce “An kama jami’an da ke da alhakin tsare wanda ake zargin, kuma ana ci gaba da gudanar da cikakken bincike don bankado lamarin da ya kai ga tserewa daga tsare shi bisa ka’ida.”

A halin yanzu, Binance a cikin martani ga ci gaban ya ce amincin Manajan sa ya kasance babban fifiko.
Kamfanin ya jaddada cewa yana aiki tare da hukumomin Najeriya don magance matsalar.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp