Ofishin masu ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, ONSA, ya tabbatar da tserewar Manajan Binance na Afirka, Nadeem Anjarwalla.
Rahotanni na cewa Anjarwalla, Manaja na yankin Afirka na Binance, ya tsere daga tsare a ranar 22 ga Maris, 2024, daga wani masaukin baki na Abuja, inda aka tsare shi da abokin aikinsa, Tigran Gambaryan bisa zargin kin biyan haraji.
Wata sanarwa da shugaban sashen yada labarai na ONSA, Zakari Mijinyawa ya fitar, ta ce Anjarwalla ya tsere daga Najeriya ta hanyar amfani da fasfo na bogi.
Mijinyawa ya ce an kama jami’an da ke da alhakin tsare wanda ake zargin kuma an fara bincike.
“Bincike na farko ya nuna cewa Mista Anjarwalla ya tsere daga Najeriya ta hanyar amfani da fasfo na bogi”.
Sanarwar ta ce “An kama jami’an da ke da alhakin tsare wanda ake zargin, kuma ana ci gaba da gudanar da cikakken bincike don bankado lamarin da ya kai ga tserewa daga tsare shi bisa ka’ida.”
A halin yanzu, Binance a cikin martani ga ci gaban ya ce amincin Manajan sa ya kasance babban fifiko.
Kamfanin ya jaddada cewa yana aiki tare da hukumomin Najeriya don magance matsalar.