fidelitybank

Man fetur ya ragu a Najeriya sakamakon a na shanye shi

Date:

Hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya, NMDPRA ta ce yawan man da ake amfani da shi a ƙasar a kowacce rana ya ragu zuwa lita miliyan 46.34, sakamakon cire tallafin man fetur da gwamnatin ƙasar ta yi.

Shugaban hukumar, Ahmed Farouk, ne ya bayyana haka a lokacin taron masu ruwa da tsaki kan harkokin albarkatun man fetur da iskar gas a birnin Legas, kamar yadda kamfanin dillancin labaran ƙasar NAN ya ruwaito.

Ya ƙara da cewa raguwar ta kai kashi 35 cikin 100 idan aka kwatanta da lita miliyan 65 da ake amfani da shi a kowacce rana kafin cire tallafin man fetur ɗin.

Ahmed Farouk ya ce ”a watan Janairu fabrairu, an sha mai lita miliyan 62 a kowacce rana, yayin da aka sha lita miliyan 71.4 a kowace rana cikin watan Maris, sai Afiru da aka sha lita miliyan 67.7 a kowacce rana, sai watan Mayu da aka sha lita miliyan 49.5 a kowace rana, sai kuma watan Yuli da ake shan lita miliyan 46.3 a kowace rana”.

Shugaban hukumar ya kuma gode wa ‘yan kasuwar da suka nuna sha’awarsu wajen shigar da man fetur ƙasar daga kasuwannin duniya.

Ya kara da cewa kawo yanzu kamfanoni 56 ne suka nuna sha’awarsu wajen shigo da man fetr zuwa ƙasar, yayin da kamfanoni 10 suka zaku wajen fara shigo da man.

Ahmed Farouk ya ce yanzu haka kamfanoni uku sun fara shigo da man fetur ɗin daga ƙasashen waje.

dailysun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp